• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Sunday, April 5, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Ministan Yaɗa Labarai ya karɓi baƙuncin ‘yan jaridar da aka sace

by WAKILIN MU
July 15, 2024
in Nijeriya
0
Ministan Yaɗa Labarai ya karɓi baƙuncin ‘yan jaridar da aka sace

Idris (na 3 daga hagu) da Ribadu (na 3 daga dama) tare da iyalan da aka sace

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

MINISTAN Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya yi maraba da sakin wasu ‘yan jarida biyu da aka sace daga gidajen su da ke bayan garin Kaduna a ƙarshen makon jiya.

Da yake jawabi a lokacin da ya karɓi baƙuncin ‘yan jaridun biyu, wato AbdulGafar Alabelewe na jaridar The Nation da AbdulRaheem Aodu na jaridar Blueprint, daga Mai Bai Shugaban Ƙasa Shawara kan Harkokin Tsaro (NSA), Malam Nuhu Ribadu, ministan ya yaba wa hukumomin tsaro bisa gaggawar ceto waɗanda lamarin ya shafa.

An saki ‘yan jaridar biyu tare da matar Mista Alabelewe da ‘ya’yan sa biyu.

Idris ya jajanta wa iyalan biyu, inda ya ce, “Muna matuƙar godiya da abin da kuka yi. Muna sane da cewa wannan wani ɓangare ne na ƙoƙarin da kuke yi na ganin an kuɓutar da duk waɗanda aka sace tare da sake haɗa su da iyalan su.

“Ina kira ga ‘yan Nijeriya da su ci gaba da yin imani da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu da hukumomin tsaro.”

Ya ƙara da cewa, “Hukumomin tsaron, a ƙarƙashin inuwar NSA, suna aiki tuƙuru domin ganin an kuɓutar da duk waɗanda aka sace ba tare da biyan kuɗin fansa ba.”

Da yake magana tun da farko, Malam Ribadu ya ce an ceto mutanen biyar da aka sace ne sakamakon haɗin gwiwar da hukumomin tsaron suka yi wanda ya kai ga gudanar da bincike da ceto cikin gaggawa.

Da yake mayar da martani, ɗaya daga cikin waɗanda aka ceto, Mista Alabelewe, ya gode wa Ribadu da tawagar sa bisa gaggawar da suka yi.

Ya ce, “Aikin ceton da ya fitar da mu daga cikin daji a jiya ya ba mu fata a ƙasar mu kuma ya ba mu ƙwarin gwiwar yarda da cewa gwamnati da gaske take wajen ganin ta magance wannan matsalar ta garkuwa da mutane.

“Ban taɓa tunanin cewa nan da mako guda da sace mu za mu kuɓuta ba. Muna godiya da gwamnati ta ɗauki mataki kuma ta tabbatar an sake mu.”

Loading

Tags: 'yan ta'addaMohammed IdrisNuhu Ribadurashin tsaro
Previous Post

Ɗan Kannywood, Ibrahim Wassh ya samu Zahra

Next Post

Jarumin Kannywood Ali Rabi’u Ali ya aurar da babbar ‘yar sa Saudat

Related Posts

Yadda CBN ke tallabe da tattalin arzikin Nijeriya, yayin sa farashin ɗanyen mai ke faɗuwar-‘yan-bori a kasuwa
Nijeriya

Yadda CBN ke tallabe da tattalin arzikin Nijeriya, yayin sa farashin ɗanyen mai ke faɗuwar-‘yan-bori a kasuwa

November 7, 2025
Shirin ƙarfafa jari: CBN ya shawarci bankuna marasa ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji
Nijeriya

Shirin ƙarfafa jari: CBN ya shawarci bankuna marasa ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji

November 2, 2025
Bankin CBN ya yunƙuro: Naira ta hana dala numfashi mai ƙarfi a ƙarshen Oktoba
Nijeriya

Bankin CBN ya yunƙuro: Naira ta hana dala numfashi mai ƙarfi a ƙarshen Oktoba

November 2, 2025
Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje
Nijeriya

Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje

October 29, 2025
Tinubu ya yi adalci ga dukkan yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai
Nijeriya

Tinubu ya yi adalci ga dukkan yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai

August 31, 2025
Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar da Sababbin Cibiyoyin Maganin Ciwon Daji

July 24, 2025
Next Post
Jarumin Kannywood Ali Rabi’u Ali ya aurar da babbar ‘yar sa Saudat

Jarumin Kannywood Ali Rabi'u Ali ya aurar da babbar 'yar sa Saudat

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!