GWAWNA Abdullahi A. Sule ya bayyana cewa Jihar Nasarawa ta fi kowace jiha a Nijeriya wuraren da su ka dace a shirya fim a cikin su.
Gwamnan ya faɗi haka ne a wajen taron iyayen ƙasa na Ƙungiyar Jaruman Fim ta Nijeriya (Actors Guild of Nigeria, AGN) wanda aka yi a Abuja.
Sule, wanda ya samu wakilcin Darakta Janar na Harkokin Yaɗa Labarai a ofishin sa, Alhaji Yakubu Lamai, ya yaba wa ‘ya’yan masana’antar shirya finafinai ta Nollywood a kan yadda su ke sama wa ƙasar nan kuɗin shiga, fahimtar juna a tsakanin al’adu, amintaka a tsakanin ƙasashe da kuma yadda ta kasance ta biyu a hanyoyin samar da aikin yi da ƙarfafa arzikin ƙasa a Nijeriya, bayan aikin gona.
Bayan ya bayana cewa Nollywood masana’anta ce ta biliyoyin naira, ya kuma tuno da cewa a shekarun baya kaɗan Bankin Duniya ya zuba dalar Amurka miliyan 20 a matsayin kuɗin tallafi don haɓaka masana’anar shirya fim ta Nijeriya, wanda hakan ne ya ba Jihar Nasarawa ƙwarin gwiwa wajen yanke shawarwar ta samar da yanayin da ya dace domin haɓaka masana’antar fim.
Gwamna Sule ya ce ya kashe sama da naira biliyan 2.5 don kammala hanyar da ta tashi daga Sisin Baƙi zuwa Farin Ruwa, kuma ta na kashe kuɗi don samar da wutar lantarki a wurin da ruwa ke zubowa daga saman tsauni, da gina otal-otal da cibiyoyin wasanni da kuma ƙauyen shirya fim da ya yi daidai da kowane iri a duniya domin mashirya fim.
Gwamnan ya ce wani tsari da ya yi don haɓaka industirin fim shi ne ya haɗa hannu da gwamnatin ƙasar Faransa da Hukumar Tace Finafinai da Bidiyo ta Ƙasa (NFVCB) a ranar Litinin, 7 ga Disamba, 2020 su ka ƙaddamar da katafaren gidan sinima mai suna ‘Canal Olympia’, wanda shi ne gidan sinima mafi girma a yankin Afrika ta Yamma, a garin Karu da ke cikin Jihar Nasarawa.