MAWAƘIN Kannywood, Albashir Hamza Yareema, ya yi godiya ga Allah (s.w.t.) bayan naɗa shi Sarkin Waƙar Marafan Yamman Zazzau da aka yi a ranar Lahadi da ta gabata.
Marafan Yamman Zazzau, Alhaji Mustapha Adamu Ubaidullahi, shi ya naɗa shi tare da wasu mutum uku.
A yayin da ya ke zantawa da mujallar Fim, Albashir ya ce, “Ina yi wa Allah (s.w.t.), Maɗaukakin Sarki, Mamallakin Sammai da Ƙassai, Mai Kowa Mai Komai, godiya. Sannan kuma ina yabo da samun karamci ga fiyayyen halitta, Annabi Muhammad (s.a.w.).
“Ina godiya ga Allah a bisa wannan al’amari na karamci da ni’ima da ya yi a gare ni.
“A gaskiya, na ji daɗin wannan naɗin sosai, ta yadda babu wani abu da zan iya misaltawa da shi, domin tabbas na samu natsuwa a kan sana’a ta ta waƙa. Na ji cewa ina yin abu ne, kuma abin da ya dace.
“Na ƙara samun tabbacin abin da na ke yi abu ne wanda yake na lura da kuma daidai. Na kuma ƙara samun natsuwa a kan sana’a ta ta waƙa. Saboda yau ta dalilin waƙa ne na samu abin da na samu a ce rawanin da na ke hangen shi a wurin sarakuna iyayen mu, yau ga shi darajar waƙa na samu rawanin sarauta, sarauta kuma babba ta sarki.

“Ka ga wannan abin godiya ne ga Allah, kuma ƙara samun yaƙini ne, ba zan iya misalta irin daɗin da na ji na samun wannan nasara ba.
“Amma na yi farin ciki matuƙa. A duniyar waƙa, a lokacin da ake naɗa min wannan rawanin, na ji cewa tabbas tamkar tsuntsu ne da aka saki daga cikin keji.
“Abin da ya sa na kawo wannan misalin, kamar cewa da ina yin waƙa ne a ɗaure a cikin keji babu wata daraja, babu wata kima. Amma ranar da ake yi min wannan rawanin na san cewa an fitar da ni daga cikin wannan kejin. To ka ga abin godiya ne, abin kuma ƙara zage damtse ne da biyayya ga na gaba da mu, domin biyayya da nuna ƙauna ta kawo haka, da kuma rage son abin duniya da kwaɗayi.

“Daga ƙarshe, ina mai jan hankali ga mawaƙan mu da su zama masu yarda da abin da su ke yi da kuma fahimtar cewa lallai ba su da wani abin da ya fi masu waƙa, ita ce baiwar da Allah (s.w.t.) ya yi masu.
“Su ɗauki sana’ar da daraja da kuma kima da sakankancewa da cewa Allah shi ne mai yin komai, ba wanin Allah ba.
“Haka kuma ina mai miƙa godiya da jinjina ga mai martaba Marafan Yamman Zazzau, Alhaji Mustapha Adamu Ubaidullahi. Allah ya saka masa da alkhairi, ya kare shi daga sharrin maƙiya. Allah ya ƙara wa rawanin sa girma, ya kuma ƙara kare mutuncin sa da darajar sa.
“Ina kuma miƙa godiya ga ɗaukacin ‘yan’uwa da abokan arziki da su ka halarci taron naɗin da aka yi min. Allah ya saka da alkhairi.

“Sannan ina godiya da irin karamci da kara da ‘yan’uwa na, Abdullahi Abbas, Sadiq Ɗan Sudan, Raliya Muhammad, Maryam da kuma Rabi’at (Maama), su ka nuna min. Na gode ƙwarai da gaske.”
An dai yi taron naɗin sarautar ne ranar Lahadi, 3 ga Fabrairu, 2024 da misalin ƙarfe 12 na rana, a ƙofar gidan Marafan Yamman Zazzau.