• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Monday, April 6, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Shin Nabraska ya yi baki biyu ne kan rigimar Ganduje da Rarara?

by DAGA ABBA MUHAMMAD
November 9, 2022
in Nijeriya
0
Mustapha Badamasi (Nabraska)

Mustapha Badamasi (Nabraska)

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

HAUSAWA dai na cewa in ka san abin da za ka faɗi, ba ka san abin da za a mai da maka ba.

A cikin kwanakin nan jarumi a Kannywood kuma mai ba gwamnan Jihar Kano shawara a kan farfaganda, Mustapha Badamasi (Nabraska), ya taso mawaƙin siyasa Dauda Adamu Abdullahi Kahutu (Rarara) a gaba a kan matsalar da ke tsakanin sa da Gwamna Abdullahi Umar Ganduje da ɗan takarar zama gwamnan jihar a jam’iyyar APC, Dakta Nasiru Yusuf Gawuna.

Rikicin da ke faruwa tsakanin Rarara da gwamnatin Kano ta sa aka cire sunan mawaƙin a cikin kwamitin yaƙin neman zaɓen Bola Tinubu.

Daga jiya zuwa yau an ga wasu tagwayen bidiyo na yawo a soshiyal midiya. A na farkon an ga Nabraska na yabon Dakta Gawuna, ya na cewa, “Bai taka maka ba, bai zubar maka ba, hasali ma mutumin nan ɗan takarar gwamnan Kano, Dakta Nasiru Yusuf Gawuna, kamilin mutum ne, mai ƙima da mutunci da martaba, wanda kuma babu ƙarya, babu son zuciya, bai taɓa faɗa da kowa ba a siyasance a zahiri da mu ka sani.” 

A ɗayan bidiyon kuma an ga Nabraska ya na cin mutuncin Gawuna a lokacin ya na ɓangaren Kwankwasiyya. 

A ciki, Nabraska na cewa, “Dakta Nasiru Yusuf Gawuna, a yau jami’an tsaro su damƙe ka, su saka ka a mota, ka na roƙon su don girman Allah su buɗe ka ka fita, don ka yi ta’annati, ka yi ɓarna. Wannan abu abin baƙin ciki ne, abu ne wanda ba iya Jihar Kano za a zaga ba, arewacin Nijeriya ma za a zaga, za a ce mu na da shugabanni daƙiƙai, jahilai, wanda ba su san me su ke yi ba.

“Me ya sa mu ke da ɗabi’a, wasu su ke da ɗabi’a ko wani ya ke da ɗabi’a irin ta dabbobi da tinkiyoyi?”

Waɗannan ba su ba ne iya bidiyoyin da Nabraska ya yi ya na yabon gwamnan Kano da ɗan takarar zama gwamnan ba. Haka kuma ba iya bidiyon da ya yi ya na cin mutuncin su ba a lokacin da baya tare da su a siyasance.

A duk lokacin da jarumin ya saki bidiyo ya na magana a kan Rarara ko gwamnan Kano da ɗan takarar gwamna, sai an fitar da wanda ya ci mutuncin su a baya. 

Wannan kuma na fitowa ne daga shafukan mai taimaka wa Rarara a ɓangaren soshiyal midiya, Rabi’u Garba Gaya, wanda shi ke maida wa Nabraska da martani a duk lokacin da ya taɓa ubangidan sa.

Hakan na nuna cewa a yanzu Nabraska ya samu damar da zai lashe dukkan aman da ya yi a baya.

Loading

Previous Post

Zaɓen 2023: An naɗa Ali Nuhu, Afakallah, Sani Mu’azu, Amart da wasu ‘yan Kannywood mayaƙan Tinubu

Next Post

Zaɓen 2023: Atiku ya mai da hankali kan kamfen, ya rabu da su Wike ‘yan bulkara – Rundunar Yaƙin Atiku

Related Posts

Yadda CBN ke tallabe da tattalin arzikin Nijeriya, yayin sa farashin ɗanyen mai ke faɗuwar-‘yan-bori a kasuwa
Nijeriya

Yadda CBN ke tallabe da tattalin arzikin Nijeriya, yayin sa farashin ɗanyen mai ke faɗuwar-‘yan-bori a kasuwa

November 7, 2025
Shirin ƙarfafa jari: CBN ya shawarci bankuna marasa ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji
Nijeriya

Shirin ƙarfafa jari: CBN ya shawarci bankuna marasa ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji

November 2, 2025
Bankin CBN ya yunƙuro: Naira ta hana dala numfashi mai ƙarfi a ƙarshen Oktoba
Nijeriya

Bankin CBN ya yunƙuro: Naira ta hana dala numfashi mai ƙarfi a ƙarshen Oktoba

November 2, 2025
Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje
Nijeriya

Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje

October 29, 2025
Tinubu ya yi adalci ga dukkan yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai
Nijeriya

Tinubu ya yi adalci ga dukkan yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai

August 31, 2025
Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar da Sababbin Cibiyoyin Maganin Ciwon Daji

July 24, 2025
Next Post
Atiku Abubakar

Zaɓen 2023: Atiku ya mai da hankali kan kamfen, ya rabu da su Wike 'yan bulkara - Rundunar Yaƙin Atiku

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!