• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Friday, June 6, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Shugabancin ƙasa: Atiku ya yi alƙawarin fara sauya fasalin Nijeriya daga ranar da za a rantsar da shi

by DAGA WAKILIN MU
December 9, 2022
in Nijeriya
0
Hagu zuwa dama: Atiku Abubakar, mataimakin takarar sa, Gwamna Ifeanyi Okowa na Jihar Delta, da Gwamna Ademola Adeleke na Jihar Osun a wajen taron

Hagu zuwa dama: Atiku Abubakar, mataimakin takarar sa, Gwamna Ifeanyi Okowa na Jihar Delta, da Gwamna Ademola Adeleke na Jihar Osun a wajen taron

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

ƊAN takarar shugabancin ƙasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar, ya sha alwashin fara sauya fasalin Nijeriya daga ranar da ya zama shugaban ƙasa a 2023, idan ya yi nasarar lashe zaɓen.

Atiku, Wazirin Adamawa, ya yi wannan alƙawarin ne a Osogbo, babban birnin Jihar Osun, lokacin da ya ƙaddamar da kamfen ɗin PDP a can.

Ya ce zai yi amfani da ajandar sa ta sauya fasalin Nijeriya domin ya kawo ƙarshen matsalar tsaro da sauran ƙalubalen da ƙasar nan ta ke fama da fuskanta.

Ya ce daga lokacin da aka gama rantsar da shi zai fara aiwatar da ayyukan raya ƙasa ta hanyar sake fasalin Nijeriya.

Wazirin ya ce: “Babban muradin mu shi ne mu tabbatar mun kawar da dukkan matsalolin rashin tsaro, rarrabuwar kai, kawar da danne haƙƙin tattalin arzikin jama’a da samar da aikin yi ga matasa. Ina ɗaukar maku alƙawarin cewa tun daga ranar da aka naɗa ni shugaba idan na yi nasara a zaɓen 2023, zan aiwatar da su.” 

Atiku ya roƙi al’ummar Osun da su jefa masa ƙuri’un su domin ya cimma burin sa na ceto Nijeriya daga mawuyacin halin da ya ce mulkin APC ya jefa ƙasar.

Ya ce: “Ba za mu kunyata ku ba, kuma ba za mu ci amanar ku kamar yadda APC ta ci amanar ku ba, saboda mu na da ƙwarewa da irin gogewar da Nijeriya ke matuƙar buƙata.”

Gwamna Ademola Adeleke, wanda aka rantsar kwanan nan, ya bayyana Atiku Abubakar a matsayin gogagge kuma mai ƙwarewar da zai iya ceto Nijeriya, har ya magance matsaloli da ƙalubalen da su ka dabaibaye ta.

Loading

Tags: Ademola AdelekeAPCAtiku AbubakarIfeanyi OkowaOsogboOsunPDPshugabancin ƙasayaƙin neman zaɓeZaɓen 2023
Previous Post

Batun ‘mutuwar’ Kannywood: Darakta Hafizu Bello ya yi wa Salisu Officer martani

Next Post

Shekara 8 da rasuwa: Hannafi ɗan Ibro ya gode da addu’a, ya nemi a ci gaba da roƙa wa mahaifin sa gafara

Related Posts

Gwamnatin Tarayya za ta tallafa wa yekuwar rigakafin cutar ƙyandar Jamus
Nijeriya

Gwamnatin Tarayya za ta tallafa wa yekuwar rigakafin cutar ƙyandar Jamus

June 4, 2025
Tinubu ya tura wakilai zuwa Neja kan ambaliyar Mokwa da ta halaka sama da mutum 150
Nijeriya

Tinubu ya tura wakilai zuwa Neja kan ambaliyar Mokwa da ta halaka sama da mutum 150

May 31, 2025
Gwamnatin Nijeriya ta goyi bayan amfani da Ƙirƙirarrar Basira cikin ɗa’a a aikin jarida – Idris
Nijeriya

Gwamnatin Tarayya ta yi ta’aziyyar mutanen da suka rasu a ambaliyar garin Mokwa

May 30, 2025
Babu wasu masu juya Tinubu ta bayan fage – Idris
Nijeriya

Babu wasu masu juya Tinubu ta bayan fage – Idris

May 25, 2025
Shirye-shiryen Shugaba Tinubu Suna Buɗe Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya – Idris
Nijeriya

Shirye-shiryen Shugaba Tinubu Suna Buɗe Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya – Idris

May 20, 2025
Idris ya ƙaryata ji-ta-ji-tar an mayar da taron bayanin ministoci zuwa London
Nijeriya

Idris ya ƙaryata ji-ta-ji-tar an mayar da taron bayanin ministoci zuwa London

May 16, 2025
Next Post
Marigayi Alhaji Rabilu Musa Ɗanlasan (Ibro)

Shekara 8 da rasuwa: Hannafi ɗan Ibro ya gode da addu'a, ya nemi a ci gaba da roƙa wa mahaifin sa gafara

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!