• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Thursday, June 12, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Zaɓen Abuja: INEC ta bada tabbacin gudanar da zaɓe mai nagarta

by DAGA WAKILIN MU
February 4, 2022
in Nijeriya
0
Sabuwar rajistar zaɓe: An samu mutum miliyan 5.35
0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

HUKUMAR Zaɓe ta Ƙasa (INEC) mai ofis a Ƙaramar Hukumar Kuje da ke Gundumar Birnin Tarayya (FCT) ta bayar da tabbaci ga masu zaɓe cewa za ta tabbatar da inganci da adalci a zaɓen ƙananan hukumomi da za a yi a yankin kwanan nan.

Idan ba a manta ba, za a gudanar da zaɓen ciyamomi da kansiloli a gundumar ta FCT ne a ranar 12 ga wannan watan na Fabrairu.

Jami’ar Zaɓe ta INEC mai kula da yankin Kuje, Madam Zainab Gbefwi, ita ce ta bayar da wannan tabbacin a lokacin da ta yi hira da Hukumar Dillancin Labarai ta Nijeriya a ranar Alhamis, a wajen wani taron horaswa da aka shirya wa ma’aikatan wucin-gadi na zaɓen.

Zainab Gbefwi ta ce hukumar za ta yi amfani da dukkan ma’aikata da kayan aiki da kuma ƙwarewar ta wajen tabbatar da cewa an yi zaɓe fisabilillahi, mai nagarta kuma wanda kowa zai yi na’am da shi.

Ta ce, “Kamar yadda Dokar Zaɓe da kuma Tsarin Mulki na 1999 su ka tanadar, haƙƙin jama’ar ƙasa ne su samu katin zaɓe kuma su zaɓi ‘yan takarar da su ke so.

“’Yan takarar su na da babbar rawar da za su taka ta hanyar yin nagana da magoya bayan su don su yi ɗabi’a mai kyau kuma su ja kunnen su dangane da haɗari da matsalolin da ke tattare da aikata maguɗin zaɓe.

“Wannan kiran ya na da muhimmanci domin ban da ƙara ƙarfi wajen zaɓe, shi kaɗai ne kuma   makamin da masu zaɓe za su iya yin amfani da shi wajen zaɓa wa kan su shugabanni.”

Haka kuma ta yi kira ga ‘yan takara da magoya bayan su da masu zaɓe da su tabbatar da cewa sun kiyaye dukkan ƙa’idojin kare kai daga cutar korona (COVID-19) a rumfunan zaɓe a lokacin zaɓen.

Kuma ta yi kira ga ‘yan takara da magoya bayan su da su kiyayi aikata duk wani abu da ya shafi maguɗin zaɓe don a tabbatar da gudanar da zaɓe mai nagarta a cikin kwanciyar hankali saboda a ciyar da mulkin dimokiraɗiyya gaba a ƙasar nan.

Wata daga cikin ma’aikatan da aka horas ɗin, Juliet Nuhu, ta faɗa wa wakilin NAN cewa za ta tabbatar da an yi ɗa’a da doka a lokacin zaɓen a Kuje.

Wakilin NAN ya ruwaito cewa yawancin ma’aikatan wucin-gadi da su ka halarci taron horaswar ‘yan bautar ƙasa ne, wato NYSC, da kuma malaman makaranta da masu neman aiki waɗanda su ka kammala karatun jami’a.

Loading

Tags: Covid-19cutar koronaFCT pollsHukumar Zaɓe ta ƘasaINECKujeZainab Gbefwi
Previous Post

Tsaron Arewa: Mamallaka gidajen rediyo da talbijin sun ƙaddamar da yekuwar yaƙi da rashin tsaro

Next Post

Sakamakon ƙazafi: Kotu ta kulle Sadiya Haruna wata 6 a kurkuku

Related Posts

Gwamnatin Tarayya za ta tallafa wa yekuwar rigakafin cutar ƙyandar Jamus
Nijeriya

Gwamnatin Tarayya za ta tallafa wa yekuwar rigakafin cutar ƙyandar Jamus

June 4, 2025
Tinubu ya tura wakilai zuwa Neja kan ambaliyar Mokwa da ta halaka sama da mutum 150
Nijeriya

Tinubu ya tura wakilai zuwa Neja kan ambaliyar Mokwa da ta halaka sama da mutum 150

May 31, 2025
Gwamnatin Nijeriya ta goyi bayan amfani da Ƙirƙirarrar Basira cikin ɗa’a a aikin jarida – Idris
Nijeriya

Gwamnatin Tarayya ta yi ta’aziyyar mutanen da suka rasu a ambaliyar garin Mokwa

May 30, 2025
Babu wasu masu juya Tinubu ta bayan fage – Idris
Nijeriya

Babu wasu masu juya Tinubu ta bayan fage – Idris

May 25, 2025
Shirye-shiryen Shugaba Tinubu Suna Buɗe Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya – Idris
Nijeriya

Shirye-shiryen Shugaba Tinubu Suna Buɗe Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya – Idris

May 20, 2025
Idris ya ƙaryata ji-ta-ji-tar an mayar da taron bayanin ministoci zuwa London
Nijeriya

Idris ya ƙaryata ji-ta-ji-tar an mayar da taron bayanin ministoci zuwa London

May 16, 2025
Next Post
Sadiya Haruna ta na tallar wani mai a cikin wani bidiyo kwanan nan

Sakamakon ƙazafi: Kotu ta kulle Sadiya Haruna wata 6 a kurkuku

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!