• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Friday, June 6, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Zaɓen 2023: INEC ta bayyana ranakun rufe karɓar sunayen ‘yan takara

by DAGA WAKILIN MU
June 10, 2022
in Nijeriya
0
Farfesa Mahmood Yakubu

Farfesa Mahmood Yakubu

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

HUKUMAR Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta gargaɗi jam’iyyu cewa za ta rufe rumbun ta na intanet (portal) inda ta ke tattara sunayen ‘yan takarar zaɓuɓɓukan 2023 a ranakun 17 ga Yuni da kuma 15 ga Yuli.

Ta ce za ta rufe karɓar sunayen ‘yan takarar zaɓen shugaban ƙasa da mataimakin sa, sanatoci da wakilan tarayya a ranar 17 ga Yuni, sai sunayen ‘yan takarar gwamna da na mataimakan su da kuma sunayen ‘yan takarar majalisun dokoki, waɗanda za a rufe karɓar su a ranar 15 ga Yuli.

Shugaban hukumar, Farfesa Mahmood Yakubu, shi ne ya yi wannan gargaɗin a lokacin da ya ke ganawa da Kwamishinonin Zaɓe na Tarayya a ranar Alhamis a Abuja.

Yakubu ya tunatar da su cewa an kammala zaɓuɓɓukan fidda gwani na dukkan jam’iyyun da za su shiga takarar zaɓen 2023 tun a ranar 9 ga Yuni.

Ya ce: “INEC na buƙatar a damƙa mata sunayen ‘yan takarar shugaban ƙasa da mataimakin sa da na sanatoci da membobin Majalisar Tarayya daga ranar 10 ga Yuni zuwa Juma’a, 17 ga Yuni.

“INEC na buƙatar sunayen ‘yan takarar gwamna da mataimakin sa da sunayen ‘yan majalisar dokoki daga ranar 1 ga Yuli zuwa 15 ga Yuli.

“Za a loda sunayen ne a cikin rumbun tattara sunayen ‘yan takarar zaɓen 2023 na intanet, wato ‘portal’.”

Yakubu ya ƙara da cewa INEC na buƙatar jami’ai huɗu na daga cikin kowace jam’iyya 18 da za su yi takara su loda sunan ɗan takarar su a cikin rumbun tattara sunayen.

Ya ce tuni INEC ta damƙa wa kowace jam’iyya lambobin ɗan makullin da ake buɗe rumbun da su domin su shiga su loda sunayen ‘yan takarar su.

“Mu na ƙara jaddada cewa sai sunayen ‘yan takarar da su ka yi nasarar lashe zaɓen fidda gwani bisa tsarin da Sashe na 84 na Dokar Zaɓe ta 2023 ne kaɗai za a loda sunayen su a cikin rumbun,” inji shi.

Loading

Tags: 'yan takaraDokar ZaɓeFarfesa Mahmood YakubuINECintanetjam'iyyun siyasa.portalzaɓe
Previous Post

Cewar minista Sadiya ga ɗaliban shirin ‘N-Build’ 40,000 da aka yaye: Horaswar da ku ka samu za ta taimaki rayuwar ku a ko’ina

Next Post

Tinubu na cikin tsaka-mai-wuya

Related Posts

Gwamnatin Tarayya za ta tallafa wa yekuwar rigakafin cutar ƙyandar Jamus
Nijeriya

Gwamnatin Tarayya za ta tallafa wa yekuwar rigakafin cutar ƙyandar Jamus

June 4, 2025
Tinubu ya tura wakilai zuwa Neja kan ambaliyar Mokwa da ta halaka sama da mutum 150
Nijeriya

Tinubu ya tura wakilai zuwa Neja kan ambaliyar Mokwa da ta halaka sama da mutum 150

May 31, 2025
Gwamnatin Nijeriya ta goyi bayan amfani da Ƙirƙirarrar Basira cikin ɗa’a a aikin jarida – Idris
Nijeriya

Gwamnatin Tarayya ta yi ta’aziyyar mutanen da suka rasu a ambaliyar garin Mokwa

May 30, 2025
Babu wasu masu juya Tinubu ta bayan fage – Idris
Nijeriya

Babu wasu masu juya Tinubu ta bayan fage – Idris

May 25, 2025
Shirye-shiryen Shugaba Tinubu Suna Buɗe Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya – Idris
Nijeriya

Shirye-shiryen Shugaba Tinubu Suna Buɗe Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya – Idris

May 20, 2025
Idris ya ƙaryata ji-ta-ji-tar an mayar da taron bayanin ministoci zuwa London
Nijeriya

Idris ya ƙaryata ji-ta-ji-tar an mayar da taron bayanin ministoci zuwa London

May 16, 2025
Next Post
Shugaba Bola Ahmed Tinubu

Tinubu na cikin tsaka-mai-wuya

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!