ƘUNGIYAR Gamayyar Marubuta da Manazarta Waƙoƙin Hausa, reshen Jihar Kano, ta shirya wa marubutan da ke jihar gasar rubuta waƙar Hausa a kan illar fyaɗe.
A yayin da ya ke bayyana fasalin duk waƙar da za a shiga gasar da ita, jam’in hulɗa da jama’a na ƙungiyar, Yasir Kallah, ya ce tilas ne a yi wa ƙasidar da za a shiga gasar da ita take da, “Jigo: Illolin Fyaɗe da Yadda Za A Magance Shi”.
Haka kuma ana so baitin waƙar ya kama daga 10 zuwa 15.
Bugu da ƙari, a sanarwar ta Yasir wadda mujallar ta gani, an ce ana so zubi da tsarin waƙar ya kasance mai ƙwar uku ce, wato Salasiyya, ko ƙwar huɗu, Ruba’iyya.
Yasir ya bayyana cewa za a duba ƙa’idojin rubutun Hausa, sannan ana so kowane sha’iri ya sanya lambar wayar sa da adireshin unguwa da garin da ya ke a takardar sa ta shiga gasar.
“Sannan ba a yarda wani ya rubuta wa wani ba; kowa tasa ta fisshe shi!” inji shi.
Wata ƙa’idar ita ce idan an kammala rubutawa sai a tura ga lambar Whastapp kamar haka 08060651676.
Jami’in ya ce za a rufe shiga gasar a ranar 28 ga Fabrairu, 2022.
Ya yi gargaɗin cewa saɓa wa ɗaya daga cikin ƙa’idojin da aka gindaya na iya sabbaba cire mawaƙi daga gasar.
Kuma ya ce: “Akwai takardun shaida da kyaututtuka na musamman ga zakarun gasar.”
A cewar Yasir, ƙungiyar za ta riƙa shirya irin wannan gasar a duk bayan wata uku.
“Kuma gasar ta ‘yan Kano ce zalla,” inji shi.
Ya kuma bayyana cewa, “Dukkanin wasu karin bayanai da sanarwa a kan gasar a duba shafin ƙungiyar na Facebook.”