• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Thursday, July 17, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Ƙungiyar Annur ta karrama furodusa Mansurah Isah

by MUKHTAR YAKUBU
December 16, 2024
in Labarai
0
Ƙungiyar Annur ta karrama furodusa Mansurah Isah
0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

 

WATA ƙungiyar addinin Musulunci ta naɗa furodusa kuma tsohuwar jarumar Kannywood, Mansurah Isah, a matsayin uwar marayun ƙungiyar Musulmi ta NASFAT tare da ba ta kambun girmamawa.

Ƙungiyar, mai suna Annur the Light of Islamic Teachings, ta naɗa jarumar ne tare da karramawar a wani taro da ta gudanar a ranar Asabar, 14 ga Disamba a ofishin ta da ke Titin Abeokuta cikin Sabon Garin Kano.

Ƙungiyar ta bai wa Mansurah muƙamin saboda irin gudunmawar da take yi wa marayu na ba su abinci da sutura da kuma kula da lafiya, da sauran abubuwa na buƙatun yau da kullum.

Mansurah ta nuna farin cikin ta da irin wannan abin alheri da aka yi mata da aka zaɓo ta daga cikin ɗimbin jama’a aka ba ta wannan matsayi da kuma karramawa.

A cewar ta, “Wannan wani al’amari ne na Allah, da yake yi wa bayin sa baiwa ta inda ya so, don haka ina godiya a gare shi. Kuma ina godiya ga ita ƙungiyar Annur da suka ga abubuwan da nake yi na alheri suka ba ni wannan kambu na girmamawa.”

Ta ƙara da cewa, “Wannan ya ƙara mini ƙaimi a kan abin da nake yi na taimaka wa mutane wajen samar musu da rayuwa mai kyau da inganci.

“Kuma ina roƙon Allah da ya ƙara ba ni damar faɗaɗa abin da nake yi har ya fi wanda aka gani a baya.

“Kuma ina roƙon Allah ya zama duk abin da zan yi ya zama ina yi ne domin sa.”

Mansurah ta samu ‘yan rakiya cikin ƙawayen ta da kuma abokan arziki, waɗanda suka haɗa da Saddika J Sarki, Jamila Gamdare, Ladidi Tubles, Fati Sulaiman, da Nura Mado.

Loading

Previous Post

Mawaƙi Abdul Respect ya zama angon Hassana Abubakar

Next Post

Za a ƙarfafa gyare-gyaren tsarin tattalin arziki da Tinubu ke yi a 2025, inji Ministan Yaɗa Labarai

Related Posts

Hukumar Shari’a da Hukumar Tace Finafinai za su haɗa gwiwa don tsaftace tarbiyya a Kano
Labarai

Hukumar Shari’a da Hukumar Tace Finafinai za su haɗa gwiwa don tsaftace tarbiyya a Kano

July 11, 2025
Labarai

Jarumin Kannywood, Baba Ƙarami ya yi magana kan ganin sa da aka yi kan keken guragu 

July 10, 2025
Tsohuwar jarumar Kannywood, Halisa tana neman addu’a
Labarai

Tsohuwar jarumar Kannywood, Halisa tana neman addu’a

July 9, 2025
Mawaƙin Manzon Allah, Abdullahi Ɗan Gano ya rasu
Labarai

Mawaƙin Manzon Allah, Abdullahi Ɗan Gano ya rasu

July 7, 2025
MOPPAN ta yi wa al’ummar Kano ta’aziyyar Aminu Ɗantata 
Labarai

MOPPAN ta yi wa al’ummar Kano ta’aziyyar Aminu Ɗantata 

June 29, 2025
Ƙungiyoyin harkar fim, KAFIGAN da MOPPAN, sun yi wa Rahama Sadau ta’aziyyar rasuwar mahaifin ta
Labarai

Ƙungiyoyin harkar fim, KAFIGAN da MOPPAN, sun yi wa Rahama Sadau ta’aziyyar rasuwar mahaifin ta

June 23, 2025
Next Post
Za a ƙarfafa gyare-gyaren tsarin tattalin arziki da Tinubu ke yi a 2025, inji Ministan Yaɗa Labarai

Za a ƙarfafa gyare-gyaren tsarin tattalin arziki da Tinubu ke yi a 2025, inji Ministan Yaɗa Labarai

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!