• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Wednesday, July 9, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Ƙungiyoyi sun buƙaci bayanai daga ‘yan sanda kan harin da aka kai fadar Sarkin Kano

by Ƙungiyoyi
July 8, 2025
in Nijeriya
0
Ƙungiyoyi sun buƙaci bayanai daga ‘yan sanda kan harin da aka kai fadar Sarkin Kano

Mai Martaba Sarkin Kano, Dakta Muhammadu Sanusi II, yana limancin sallar Idi

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

A CIKIN sa’o’i 24 bayan harin da aka kai fadar Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II, da ke Gidan Rumfa, Ƙofar Kudu, a cikin birnin Kano, wasu ƙungiyoyin farar hula da ke ƙarƙashin jagorancin One Kano Agenda, sun buƙaci a hukumomin tsaro, musamman ‘yan sanda, da su fitar da bayani kan shiru da suka yi game da lamarin.

An ruwaito cewa wata tawagar tsohon Sarkin Kano, Alhaji Aminu Ado Bayero, ce ta kai harin a daren Lahadi, a yayin da take dawowa daga gidan marigayi attajirin Kano, Alhaji Aminu Alhassan Ɗantata, bayan kai gaisuwar ta’aziyya.

Bayanan da ƙungiyoyin suka tattara dai sun yi nuni da cewar tsohon sarkin ya bar hanyarsa ta yau da kullum da ke kai shi Mandawari, ya karkata ta Kabara wadda ke gaban fadar Gidan Rumfa, wanda hakan ya janyo harin da wasu da ake zargin na cikin ‘yan rakiyar sa ne suka kai.

Ƙungiyoyin farar hular da suka haɗa kai ƙarƙashin jagorancin One Kano Agenda, sun bayyana shiru da jam’ian tsaro suka yi a matsayin abu mai tayar da hankali wanda ke nuna gazawa wajen tabbatar da zaman lafiya a jihar, kuma yana iya haifar da ruɗani da fitina.

Sun ce hakan na iya zama wani yunƙuri na daban don Kawo Rashin Zaman Lafiya da gangan a Jihar Kano.

Ƙungiyoyin sun kuma bayyana Rahoton Abubuwan Da Aka Lalata da Wanda Aka Sata Kamar Haka :

Motocin ‘Yan Sanda:

Hilux ta ‘yan sanda (NPF 182D) – Mopol 9.

Hilux ta ‘yan sanda (NPF 195D) – Mopol 52.

Abubuwan da aka lalata:

Babur na Abdullahi Shehu (Jami’in ‘yan sanda)

Babur na Ibrahim Isa (Mashal din tsaro a masarautar)

Babbar ƙofa ta ƙarfe ta masarautar ta lalace matuƙa.

Wurin tsaron ‘yan sanda da ke fadar Shima an lalata shi.

Kayan Tsaro da Aka Sata:

Cikakken kayan ‘yan sanda na kamfale.

Takalman tsaro na ‘yan sanda guda ɗaya.

Majigin harsashi ɗaya – wanda ke da matuƙar hatsari.

Mutanen da suka jikkata:

Maigoma Ɗan’agundi (yana kwance a Asibitin Murtala Muhammed).

Yunusa Babba (Mashal ɗin tsaro).

Murtala Muhammed (Jami’in ‘yan sanda na musamman).

Abin da muke buƙata:

1. A gaggauta fara bincike kan harin da aka kai, Sannan a yi nazari akan abin da aka lalata kamar dukiyoyin gwamnati da kuma kai hari ga jami’an tsaro da fararen hula.

2. A gano, a kama, sannan a gurfanar da duk masu hannu akan kai wannan hari.

3. A nemo kayan ‘yan sanda da aka sata, musamman majigin harsashi wanda ke da babbar barazana ga tsaro.

4. A ƙara tsaurara tsaro a fadar Sarkin Kano Muhammadu Sanusi II da ma gidansa baki ɗaya.

Muna kira ga hukumomin tsaro a Kano da su ɗauki matakin gaggawa da na kwarjini don kare doka da oda, da tabbatar da zaman lafiya a jihar.

Doka ba za ta amince da aikata laifi ba, kuma babu wanda ya fi doka, ko da kuwa yana da matsayin mulki ko iko.

Waɗanda suka rattaba hannu:

Mustapha Abdullahi – Kano Digital Media Rangers.

Comrade Salisu Gambo – Youth Mobilization By Media.

Alhaji Suleiman Idris – Northern Youth Assembly.

Malam Abdulƙadir Abubakar – One Voice Development Initiative.

Aisha Muhammad Shettima – Beyond Border Alliance.

Barr. Badamasi Gandu – Kano First Forum.

Amb. Abbas Abdullahi – Shugaban One Kano Agenda.

Barr. Mukhtar Musa – Sakataren One Kano Agenda.

Loading

Previous Post

Mawaƙin Manzon Allah, Abdullahi Ɗan Gano ya rasu

Next Post

Tinubu ba zai yarda hayaniyar siyasar 2027 ta ɗauke masa hankali ba – Minista

Related Posts

Ministoci za su fara gabatar da rahoton ayyuka a taron manema labarai
Nijeriya

Tinubu ba zai yarda hayaniyar siyasar 2027 ta ɗauke masa hankali ba – Minista

July 8, 2025
SHEKARA ƊAYA BAYAN KOMAWA KAN KARAGAR MULKI: Tasirin Yadda Mai Martaba Khalifa Muhammadu Sanusi II Ya Dawo Da Martabar Masarautar Kano
Nijeriya

SHEKARA ƊAYA BAYAN KOMAWA KAN KARAGAR MULKI: Tasirin Yadda Mai Martaba Khalifa Muhammadu Sanusi II Ya Dawo Da Martabar Masarautar Kano

July 5, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya da Ɗangote sun halarci jana’izar Aminu Ɗantata a Saudiyya
Nijeriya

Tawagar Gwamnatin Tarayya da Ɗangote sun halarci jana’izar Aminu Ɗantata a Saudiyya

July 1, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya ta miƙa saƙon ta’aziyya daga Tinubu tare da yin addu’o’i a gidan Ɗantata a Madina
Nijeriya

Tawagar Gwamnatin Tarayya ta miƙa saƙon ta’aziyya daga Tinubu tare da yin addu’o’i a gidan Ɗantata a Madina

June 30, 2025
Nijeriya

Gwamnatin Tarayya ta bada tabbacin akwai tsaro a Abuja duk da gargaɗin da Amurka ta ba matafiya

June 23, 2025
Kiran Gwamnatin Tarayya ga ‘yan jarida: Ku zama jigo wajen gina dimokiraɗiyyar Nijeriya
Nijeriya

Kiran Gwamnatin Tarayya ga ‘yan jarida: Ku zama jigo wajen gina dimokiraɗiyyar Nijeriya

June 21, 2025
Next Post
Ministoci za su fara gabatar da rahoton ayyuka a taron manema labarai

Tinubu ba zai yarda hayaniyar siyasar 2027 ta ɗauke masa hankali ba – Minista

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!