Yayin da ya rage saura wata ɗaya a fara yaƙin neman zaɓen shugaban ƙasa, sanatoci da na mambobin Majalisar Tarayya, Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta gargaɗi jam’iyyu da ‘yan takara da su guji take dokoki, musamman waɗanda ta haramta a lokacin kamfen.
Daraktan Yaɗa Labarai na hukumar, Mista Festus Okoye, shi ne ya bayyana haka a cikin wata hira da jaridar Punch ta yi da shi a ƙarshen makon da ya gabata.
Za a fara yaƙin neman zaɓe ne a ranar 28 ga Satumba, 2022, yayin da za a yi zaɓen shugaban ƙasa da na ‘yan Majalisar Tarayya a ranar 25 ga Fabrairu, 2023.
Okoye ya bayyana cewa wuraren da dokar INEC ta hana yin kamfen da tarurrukan siyasa sun haɗa da coci-coci, masallatai, gine-gine da ofisoshin Gwamnatin Tarayya na jihohi ko ƙananan hukumomi da kuma amfani da mutum-mutumin ‘masquarade’.
Ya ce ya zama wajibi jam’iyyu da ‘yan takara su bi ƙa’idojin da Dokar Zaɓe ta 2022, Sashe na 92, ta gindaya.
Daga cikin sharuɗɗan da daraktan ya jaddada akwai “yin hani da amfani da mutum-mutumin domin ƙara wa taron siyasa armashi, yin amfani da wuraren ibada, ofisoshin gwamnati ko gine-ginen gwamnati domin yi wa ma’aikata kamfen da sauran su.”
Ya ce: “Sashe na 92 na Dokar Zaɓe ta 2022 ya hana rubutawa ko rera taken jam’iyya ko na ɗan takara ɗauke da kalaman zagi, cin fuska ko aibata wani ɓangaren addini, yare, ƙabila ko wani yankin jama’a.
“Ba a yarda a riƙa amfani da zage-zage a lokacin kamfen ko tarurrukan siyasa ba. Kuma ban da kalaman da ka iya harzuƙa wani ko wasu gungun jama’a su hasala har su tayar da hargitsi.
“A guji amfani da yare ana cin zarafin wani yare, kuma ban da shaguɓe da kalaman aibatawa da ka iya harzuƙa wasu su ɗauki doka a hannun su.
“Sashe na 3 na wannan doka ya haramta kamfen ko taron siyasa a wuraren ibada, ofishin ‘yan sanda, ofisoshin gwamnati da gine-ginen gwamnati. Saboda haka ba a yarda a tallata jam’iyya ko ɗan takara a waɗannan wurare ba.
“Sashe na 2(5) kuma ya haramta jam’iyya ko ɗan takara ya yi amfani da ‘yan daba ɗauke da makamai. Kada jam’iyya ko ɗan takara ya yi amfani da wasu jami’an tsaro masu zaman kan su ɗauke da makamai a wurin kamfen, taro ko wurin zaɓe.
“Sashe na 7(a) (b) da kuma Sashe na 8 sun jaddada cewa duk wanda ya karya Sashe na 92 za a yi masa tarar naira miliyan ɗaya ko ɗaurin shekara ɗaya, idan ɗan takara ne.
“Idan jam’iyya ce ta karya dokar, za a yi mata tarar naira miliyan biyu. Idan ta ƙara kuma tarar naira miliyan ɗaya.
“Wanda aka kama ya tayar da hargitsi ko ya yi amfani da makami kuma za a yi masa tarar naira 500,000 ko ɗaurin shekaru uku, ko kuma a haɗa masa duka biyun.”