SAKAMAKON cacar bakin da ake yi tsakanin Nijeriya da Jamhuriyar Nijar, wanda ya sa su ke zaman doya da man ja, fitattun mawaƙa Aminu Ladan Abubakar Ala da Fati Nijar sun jagoranci wata kalankuwa da baje-kolin waƙoƙin da su ka shafi ƙasashen biyu masu alaƙar zumunci da ‘yan’uwantaka.
Sanin kowa ne cewa sakamakon juyin mulkin da sojojin Nijar su ka yi wa Firaminista Mohammed Bazoum, Nijeriya ta yanke hulɗar diflomasiyya da Nijar kuma ta ƙaƙaba mata takunkumin tattalin arziki, a bisa wani mataki da ƙungiyar ƙasashen Afrika ta Yamma (ECOWAS) ta ɗauka.
Matakan sun haifar da rashin jituwa tsakanin mutanen Nijeriya da Nijar har ana zancen yaƙi da juna.
An yi taron na su Ala ne a ranar Asabar, 16 ga Agusta, 2023 a harabar gidan Rediyon Premier FM da ke titin filin sukuwar dawaki a Kano, kuma ya samu halartar mawaƙa da malamai da masu sarauta da sauran jama’a.
Tun da farko da ya ke jawabi a game da alaƙar ƙasashen biyu, shugaban Majalisar Malamai ta Arewa da kuma ta Jihar Kano, Sheikh Ibrahim Khalil, ya bayyana ƙasashen biyu a matsayin wani yanki da ke da alaƙar da ba za su rabu ba duk kuwa da cewa Turawa sun raba su.

Ya ce ta fuskar mu’amalar ciniki da auratayya kuma har yanzu mutane na ci gaba a matsayin mu na ‘yan’uwan da halitta ta haɗa mu, addini ya haɗa mu, yadda ya haɗa mu da sauran abubuwa tsawon tarihi, don haka waɗannan abubuwa da su ke tasowa ba za su yi tasiri ga alaƙar mu ba a matsayin mu na ‘yan’uwa.
Malamin ya yi kira da a fahimci wannan abin da ilimi da kuma basira don kada mu bar abin da zai lalata wannan kyakkyawar alaƙar ga yara masu tasowa.

Mujallar Fim ta ruwaito cewa a taron an fi mayar da hankali ga waƙoƙin da su ka shafi alaƙar ƙasashen biyu, inda mawaƙa irin su Ala, Fati Nijar, Bashir Ɗandago, Miftahu Umar, da Adam M. Kirfi kowa ya gabatar da waƙoƙin sa.
An yi taron an gama lafiya, kuma mahalarta sun nuna farin cikin su da shirya shi da aka yi.


