• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Tuesday, June 17, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Gwamnatin Kano ta dakatar da haska finafinan Kannywood 22 a intanet da talbijin 

* Matakin ya shafi Ɗakin Amarya, Labari Na, Garwashi, Daɗin Kowa, Gidan Sarauta, da Manyan Mata

by ALI KANO
May 19, 2025
in Labarai
0
Hukuma ta rufe gidajen gala a Kano har sai bayan Ramadan

Alhaji Abba El-Mustapha, Shugaban Hukumar Tace Finafinai da Ɗab'i ta Jihar Kano

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

HUKUMAR Tace Finafinai da Ɗabi’i ta Jihar Kano ta bada umarnin daina nuna finafinai masu dogon zango 22 saboda sun saɓa dokokin ta, ta ce a daina nuna su a intanet da talbijin.

A cikin wata sanarwa da jami’in yaɗa labarai na hukumar, Malam Abdullahi Sulaiman, ya fitar bayan wani taron shawara da masu ruwa da tsaki a harkar, hukumar ta ce finafinan da abin ya shafa an sake su ne ba tare da an tace su a hukumar ba.

A sanarwar, an ruwaito cewa Babban Sakataren hukumar, Alhaji Abba El-Mustapha, shi ne ya bada umurnin dakatar da haska finafinan bayan bincike ya gano cewar ana nuna finafinan bayan an yi kunnen uwar shegu da dokokin hukumar.

Sanarwar ta ce: “Finafinan da aka dakatar sun gaza bin ƙa’idojin da aka kafa na a miƙa dukkan finafinai domin su samu amincewar hukuma kafin a shirya su, tallata su, nuna su a intanet, ko haska su a talbijin.”

Finafinan da aka dakatar ɗin sun ƙunshi wasu waɗanda ke matuƙar tashe a wajen masu kallon finafinan Hausa, ciki har da Ɗakin Amarya, Labari Na, Garwashi, Daɗin Kowa, Gidan Sarauta, da Manyan Mata.

Sauran su ne Mashahuri, Wasiyya, Tawakkaltu, Miji Na, Wani Zamani, Mallaka, Kuɗin Ruwa, Boka Ko Malam, Rana Dubu, Fatake, Jamilun Jiddan, Shahadar Nabila, Tabarma, Kishiya Ta, Rigar Aro, da Wa Ya San Gobe?

Hukumar ta ce: “Tilas ne dukkan furodusoshi da mamallakan waɗannan finafinan su daina haska su a talbijin ko nuna su a intanet ba tare da ɓata lokaci ba, kuma ana buƙatar su da su miƙa finafinan nasu ga hukumar domin tacewa tsakanin ranar Litinin, 19 ga Mayu, da ranar Lahadi, 25 ga Mayu, 2025.”

Ta ƙara da cewa duk wanda ya ƙi bin wannan umurnin a cikin lokacin da aka gindaya zai fuskanci matakan shari’a.

Haka kuma hukumar ta yi kira ga kafofin watsa labarai da hukumomin kula da finafinai da su goyi bayan ta don tabbatar da tasirin dokokin tace finafinan.

“Muna kira ga tashoshin talbijin da Hukumar Kula da Gidajen Rediyo da Talbijin (NBC) da su mara wa ƙudirorin mu baya don tabbatar da an bi dokokin tace finafinai tare da haɓaka ƙwarewa a industirin Kannywood,” inji ta.

Hukumar ta jaddada sadaukarwar ta wajen tabbatar da ɗa’a da kare al’adu a cikin finafinan Hausa.

Loading

Tags: Abba El-Mustaphadakatarwadokokin tacewaHukumar Tace Finafinai Da Ɗab'i ta Jihar Kano
Previous Post

Idris ya ƙaryata ji-ta-ji-tar an mayar da taron bayanin ministoci zuwa London

Next Post

Ƙungiya ta ja kunnen gwamnatin Kano kan dakatar da finafinan Kannywood 22

Related Posts

Furodusan Kannywood, Abubakar Galadima ya zama jakaden garin sinadarin girki na Zahir Spice Curry
Labarai

Furodusan Kannywood, Abubakar Galadima ya zama jakaden garin sinadarin girki na Zahir Spice Curry

June 15, 2025
Wani maigida na ya ce wahalar banza nake yi a kan Yerima Shettima, inji Hussaini Danko
Labarai

Wani maigida na ya ce wahalar banza nake yi a kan Yerima Shettima, inji Hussaini Danko

June 13, 2025
Jarumin Kannywood, Abdul M. Shareef zai auri jaruma Maryam Malika
Labarai

Jarumin Kannywood, Abdul M. Shareef zai auri jaruma Maryam Malika

June 12, 2025
Hukumar Tace Finafinai ta Kano ta yaba wa ɗakunan taruka bisa bin doka da oda lokacin bukukuwan Sallah
Labarai

Hukumar Tace Finafinai ta Kano ta yaba wa ɗakunan taruka bisa bin doka da oda lokacin bukukuwan Sallah

June 12, 2025
Rahama Sadau ta raba barka da Sallah ga ‘yan fim na Kaduna
Labarai

Rahama Sadau ta raba barka da Sallah ga ‘yan fim na Kaduna

June 11, 2025
‘Aure tsakanin jaruman Kannywood, Mansurah da Momoh’: Yadda lamarin yake
Labarai

‘Aure tsakanin jaruman Kannywood, Mansurah da Momoh’: Yadda lamarin yake

June 11, 2025
Next Post
Ƙungiya ta ja kunnen gwamnatin Kano kan dakatar da finafinan Kannywood 22

Ƙungiya ta ja kunnen gwamnatin Kano kan dakatar da finafinan Kannywood 22

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!