A RANAR Asabar, 2 ga Satumba, 2023 aka ɗaura auren ɗiyar fitaccen marubuci kuma jarumi, Malam Ado Ahmad Gidan Dabino, MON, wato Fatima Ado Ahmad Gidan Dabino, da angon ta, Bello Umar Kawaji.
An ɗaura auren da misalin ƙarfe 11 na safe a Masallacin Juma’a na Al-Furƙan da ke unguwar Nassarawa GRA, Kano, a kan sadaki N100,000, kuma an biya lakadan kuma wakilin waliyyin amarya, Alaramma Muttaƙa Sani ya karɓa.

Wakilin mujallar Fim ya ruwaito cewa taron ɗaurin auren ya samu halartar manyan mutane kama daga sarakuna da marubuta da kuma ‘yan siyasa.
Waɗanda su ka halarta sun haɗa da Farfesa Abdalla Uba Adamu, Farfesa Yusuf Adamu, Dakta Tahir A. Ahmad Sarkin Dawaki Maituta, Kabiru Assada, Aminu Ladan Abubakar (Ala Waƙa), Zaharaddin Ibrahim Kallah, Mai Unguwar Mandawari Alhaji Ibrahim Muhammad Madawari, da Khadil Imam.

Tun kafin ranar ɗaurin auren an shirya wa amarya Fatima taron saukar karatun Alƙur’ani da addu’o’i, sannan bayan an ɗaura da yammacin ranar Asabar ɗin an yi taron addu’a na musamman a gidan Ado Ahmad Gidan Dabino domin Allah ya kawo zaman lafiya a tsakanin ango da amarya kuma ya tsare su daga dukkan fitintinu na zaman aure.
Allah ya tabbatar da hakan, amin.






Masha Allah 🤗 Allah ya bada zaman lafiya, Allah yasa albarka a wan nan auren
Comment: Ya Allah ka yi wa auren albarka amin. IN DA SO DA KAUNA…