TSOHUWAR jarumar Kannywood, Khadija Muhammad Sani, wadda aka fi sani da Khadija Yobe, ta bayyana dalilin da ya sa aka gan ta a cikin matasa masu zanga-zangar nuna takaici kan matsalar rashin tsaro da ake fama da ita a Arewa duk da yake ta yi aure.
Surutu ya baibaye sassan soshiyal midiya lokacin da aka ga hoton ta ita ma ɗauke da kwalin nuna takaici a ranar murnar samun ‘yancin kai, wato 1 ga Oktoba.
Idan kun tuna, mujallar Fim ta ba da labarin auren Khadija Yobe ko Karima ta cikin ‘Izzar So’ da angon ta, mawaƙi Izzudden M. Doko, wanda tun daga nan ba a ƙara jin ɗuriyar ta ba sai yanzu.

Ganin ta a cikin ‘yan zanga-zangar ya sa wasu mutane su na tambaya game da matsayin auren, har wasu na tunanin ko ta fito ne.
Sai dai da mujallar Fim ta nemi jin ta bakin jarumar ta waya, sai Khadija ta tabbatar mana da cewa lallai ita ce aka gani a cikin masu zanga-zangar kuma auren ta na nan daram daƙam.
A game da shigar ta zanga-zangar ta yi bayanin cewa, “Na zo Kano ne sai na samu ana yi. To ni kuma na ga abin da ya shafe ni ne, ya shafi yanki na da ƙasa ta, don haka ni ma na shiga aka yi da ni.
“Amma ba magana ce ta ko ina da aure ko ba ni da aure ba. Aure na ya na nan, ni a yanzu matar aure ce. Kuma aure ba zai hana ni na nuna ɓacin rai na da abin da ya ke faruwa a yanki na da kuma ƙasa ta ba.”
Comments 1