JARUMI a Kannywood, Haruna Shu’aibu, wanda aka fi sani da Ubale KD ko Ubalen Danja, shi ma ya zama uba.
Allah ya azurta Ubale da santalelen ɗa namiji a jiya Asabar, 21 ga Oktoba, 2023.
Amaryar sa, A’isha, ta haihu da misalin ƙarfe 2:00 na rana a wani asibitin kuɗi mai suna Nana A’isha da ke Tudun Nufawa, Kaduna.
Kamar dai yadda aka saba a wannan zamani, har an raɗa wa jariri suna Abubakar Sadeeq, ba sai an jira zuwa kwana bakwai ba.
Idan ba ku manta ba, mujallar Fim ta ba ku labarin cewa an ɗaura auren Ubale da A’isha a ranar Asabar, 1 ga Oktoba, 2022 a masallacin Juma’a na ‘Yanlilo da ke Tudun Wada, Kaduna.
Ubale da matar sa sun samu ƙaruwa bayan sun shekara ɗaya da kwana 20 cif da aure.
Allah ya raya Abubakar Sadeeq, ya kuma albarkaci rayuwar sa, amin.