SHUGABAN Kwamitin tsaftace ayyuka a Kannywood, Malam Tijjani Abdullahi (Asase), ya bayyana cewa kwamitin ya samu nasarori a ayyukan da yake yi na fita waɗanda suka haɗa da rufe wuraren da ake shirya finafinai ba bisa ƙa’ida ba guda uku tare da kama daraktoci biyu da sauran ma’aikata da jaruman masana’antar har 30.
Hukumar Tace Finafinai da Ɗab’i ta Jihar Kano ce ta kafa kwamitin don tabbatar da ana bin dokokin ta sau da ƙafa.
Asase ya shaida wa shugaban hukumar, Alhaji Abba El-Mustapha, a wani zama da suka yi, cewa abin da suka yi wata babbar nasara ce ga masana’antar.
An yi zaman ne a ranar Talata, 24 ga Yuli, 2024, inda kwamitin ya ba da rahoto kan wasu daga cikin nasarorin da suka samu tun bayan da aka naɗa su a matsayin shugabanni.
Da yake nasa jawabin, El-Mustapha ya jinjina wa ‘yan kwamitin kan yadda suka jajirce wajen sauke nauyin da hukumar ta ɗora masu bisa cancantar su tare da kishin da suke da shi na ganin hukumar da masana’antar Kannywood sun samu cigaba mai ɗorewa.
Ya jaddada cewa ba a kafa kwamitin don a ci wa kowa mutunci ba sai don a tsaftace tare da fito da ƙima da darajar masana’antar.
Ya ƙara da cewa: “Manufar kafa kwamitin ita ce tabbatar da ana bin doka da ƙa’ida a masana’antar Kannywood sau da ƙafa tare da bin duk wata hanya da ake ganin masana’antar ta samu cigaba ta yadda za ta yi gogayya da sauran takwarorin ta na Nijeriya dama duniya baki ɗaya.”
El-Mustapha ya ƙara da cewa, “Tuni lokaci ya wuce da wasu za su rinƙa amfani da sunan masana’antar ta Kannywood suna yin abin da bai kamata ba domin cimma ƙudirorin ƙashin kan su.
“Don haka ina miƙa saƙon godiya ta ga ‘yan masana’antar Kannywood da al’ummar Jihar Kano baki ɗaya dangane da goyon baya da haɗin kai tare da goyon bayan da suke bai wa hukumar a ko da yaushe.”
