• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Tuesday, August 11, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Nijeriya ta jaddada ƙudirin ƙarfafa ƙawance da Indonesiya a taron Indonesiya da Afirka

by WAKILIN MU
September 2, 2024
in Nijeriya
0
Nijeriya ta jaddada ƙudirin ƙarfafa ƙawance da Indonesiya a taron Indonesiya da Afirka

Alhaji Mohammed Idris yana gabatar da jawabin Shugaban Nijeriya a taron

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

GWAMNATIN Tarayya ta jaddada ƙudirin ta na zurfafa alaƙar ta da ƙasar Indonesiya, tare da mai da hankali kan batun tattalin arziki da kuma hanyoyin haɗin gwiwa.

An tabbatar da hakan ne a taron Indonesiya da nahiyar Afrika karo na biyu, wanda ake gudanarwa daga ranakun 1 zuwa 3 na Satumba, 2024, a Bali, babban birnin ƙasar.

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, wanda ya wakilci Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, shi ne ya jagoranci tawagar Nijeriya zuwa Babban Taron Haɗin Gwiwa na Masu Ruwa da Tsaki da kuma Taron Shugabanni a ƙasar da ke nahiyar Asiya.

Ministan ya nanata ƙudirin Nijeriya na ƙulla ƙawance da Indonesiya, yana mai cewa dukkan yankunan biyu suna da abubuwa da yawa da za su samu daga ƙara haɗin gwiwa a fannin kasuwanci, zuba jari, da musayar ilmi da ƙwarewa.

Ya ce: “Taron Indonesiya da Afirka wata hanya ce ta haɗin gwiwa, da nufin ciyar da ƙasashen mu biyu zuwa makoma mai haske da wadata.”

Idris ya ƙara da cewa, “Nijeriya ta ƙudiri aniyar yin amfani da ƙarfin da muke da shi da albarkatun mu don mai da hankali kan muhimman ginshiƙai kamar sauyin tattalin arziki, makamashi da haƙar ma’adinai, samar da abinci da lafiya, da tattalin arziki na dijital.

“Waɗannan su ne ginshiƙan da za a gina haɗin gwiwar mu a nan gaba, tare da zurfafa haɗin gwiwa da cigaban tattalin arziki mai ɗorewa wanda zai amfani dukkan al’ummomin mu.”

Taron ya jaddada gagarumin ƙarfin tattalin arziki da al’ummar Afirka da Indonesiya suke da su, waɗanda ke wakiltar sama da mutane biliyan 1.7 da jimillar ƙarfin tattalin arziki na GDP na dalar Amurka tiriliyan 4.4.

Taron ya tattaro shugabannin ƙasashe, jami’an gwamnati, ‘yan kasuwa, da masu ruwa da tsaki daga sassa daban-daban, inda suka tattauna haɗin gwiwar tattalin arziki, da magance matsalolin duniya, da kuma lalubo hanyoyin samun cigaba mai ɗorewa tare.

Jagorancin Nijeriya wajen ciyar da ajandar Tarayyar Afirka ta 2063 shi ma ya kasance jigon tattaunawa a taron.

Alhaji Mohammed Idris a wurin taron

Ministan ya yi bayani kan cikakkiyar ajandar Shugaban Ƙasa Tinubu ta sauye-sauyen tattalin arziki, tsaro, shugabanci, da cigaban al’umma a matakin ƙasa, da kuma ƙoƙarin da yake yi na inganta harkokin kasuwanci a yankin, da ababen more rayuwa, da kwanciyar hankali a siyasance ta hanyar jagorancin sa a Ƙungiyar Raya Tattalin Arziƙin Ƙasashen Yammacin Afirka (ECOWAS).

An bayyana rawar da Nijeriya ke takawa a Yankin Kasuwanci na Nahiyar Afirka (AfCFTA) a matsayin babbar hanyar bunƙasa kasuwanci da masana’antu a cikin Afirka.

Taron, wanda ya samu halartar wakilai daga ƙasashen Afirka 22 da kuma wasu ƙasashe biyar da ba na Afirka ba, ya kuma tuna da taron nahiyoyin Asiya da Afirka na shekarar 1955, wanda aka fi sani da “Bandung Spirit”, wanda ya aza harsashin dangantakar Asiya da Afirka.

Shugabanni mahalartan taron

Taron ya yi kira da a ƙara inganta yin mu’amala a tsakanin nahiyoyi ta fuskar kasuwanci, zuba jari, da haɗin gwiwar raya ƙasa.

An jaddada cewa kamata ya yi Afirka ta zarce matakin mai fitar da ɗanyen man fetur kawai, ta zama cibiyar samar da kayayyaki, tare da ba da tabbaci na musamman ga ayyukan bututun iskar gas da ke ratsa sahara tsakanin Nijeriya da Aljeriya da kuma Morokko.

Taron na Indonesiya da Afirka ya kasance wani dandali na ƙarfafa dangantakar tattalin arziki tsakanin Indonesiya da ƙasashen Afirka.

Loading

Tags: Bola Ahmed TinubuIndonesiaIndonesiyaMohammed IdrisNijeriyataron ƙasa da ƙasa
Previous Post

Nijeriya za ta ƙarfafa alaƙa da Indonesiya a taron ƙasar da Afirka karo na biyu

Next Post

Mawaƙiya a Kannywood, Maryam Fantimoti, za ta yi aure

Related Posts

Yadda CBN ke tallabe da tattalin arzikin Nijeriya, yayin sa farashin ɗanyen mai ke faɗuwar-‘yan-bori a kasuwa
Nijeriya

Yadda CBN ke tallabe da tattalin arzikin Nijeriya, yayin sa farashin ɗanyen mai ke faɗuwar-‘yan-bori a kasuwa

November 7, 2025
Shirin ƙarfafa jari: CBN ya shawarci bankuna marasa ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji
Nijeriya

Shirin ƙarfafa jari: CBN ya shawarci bankuna marasa ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji

November 2, 2025
Bankin CBN ya yunƙuro: Naira ta hana dala numfashi mai ƙarfi a ƙarshen Oktoba
Nijeriya

Bankin CBN ya yunƙuro: Naira ta hana dala numfashi mai ƙarfi a ƙarshen Oktoba

November 2, 2025
Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje
Nijeriya

Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje

October 29, 2025
Tinubu ya yi adalci ga dukkan yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai
Nijeriya

Tinubu ya yi adalci ga dukkan yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai

August 31, 2025
Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar da Sababbin Cibiyoyin Maganin Ciwon Daji

July 24, 2025
Next Post
Mawaƙiya a Kannywood, Maryam Fantimoti, za ta yi aure

Mawaƙiya a Kannywood, Maryam Fantimoti, za ta yi aure

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!