• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Wednesday, August 26, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Ƙasashe 7 sun mara wa Nijeriya baya don kafa Cibiyar Koyar da Ilimin Yaɗa Labarai ta UNESCO – Minista

by WAKILIN MU
January 22, 2025
in Nijeriya
0
Ƙasashe 7 sun mara wa Nijeriya baya don kafa Cibiyar Koyar da Ilimin Yaɗa Labarai ta UNESCO – Minista

MINISTAN Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, a tsakiyar tawagar UNESCO da NOUN

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram
Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, a tsakiyar tawagar UNESCO da NOUN

MINISTAN Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya bayyana cewa Nijeriya ta samu goyon bayan ƙasashe bakwai tare da alƙawuran ƙasashe 20 domin a kafa Cibiyar Koyar da Ilimin Yaɗa Labarai ta Duniya (IMILI) ta hukumar UNESCO.

Ita da UNESCO, ita ce Hukumar Ilimi da Kimiyya da Al’adu ta Majalisar Ɗinkin Duniya.

A Turance, IMILI na nufin International Media and Information Literacy Institute.

Da yake jawabi a Abuja a ranar Talata yayin da ya karɓi baƙuncin tawagar UNESCO da ta zo duba shirin Nijeriya na kafa cibiyar, Idris ya tabbatar da cewa Nijeriya za ta samu amincewar ƙarshe a taron UNESCO na gaba.

Ya ce: “Tuni mun samu goyon bayan ƙasashe bakwai, kuma akwai ƙasashe kimanin ashirin da suka nuna shirin su na goyon bayan Nijeriya.

“Mun tabbatar da cewa a taron UNESCO na gaba, za a ba Nijeriya damar kafa MIL a Abuja, a Buɗaɗɗiyar Jami’ar Nijeriya (NOUN).”

Ministan ya bayyana farin cikin sa da sakamako mai kyau da aka samu daga tawagar masu duba shirye-shiryen, kuma ya jaddada cewa Nijeriya ta jajirce wajen cika dukkan sharuɗɗan UNESCO na kafa cibiyar.

Minista yana jagorantar zaman da aka yi

Ya ƙara da cewa wannan shirin ba na Nijeriya kaɗai ba ne, har ma da Afrika da sauran duniya baƙi ɗaya.

Ya ce, “Cibiyar Koyar da Ilimin Yaɗa Labarai ba domin al’ummar Nijeriya kawai aka ƙirƙire ta ba, an ƙirƙire ta ne domin al’ummar duniya baki ɗaya.

“Wannan wata dama ce ga ƙasar mu ta nuna ƙwarewa, gogewa, da jajircewa kan Ilimin Yaɗa Labarai na duniya.”

Idris ya bayyana cewa Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da dukkan kuɗaɗen da ake buƙata domin kafa cibiyar, kuma ya ce Ma’aikatar Yaɗa Labarai tana aiki tare da Ma’aikatar Ilimi da sauran masu ruwa da tsaki domin tabbatar da nasarar shirin.

Ya jaddada cewa Koyar da Ilimin Watsa Labarai yana da matuƙar muhimmanci wajen yaƙi da matsalar yaɗa labaran ƙarya wanda ke barazana ga zaman lafiya da tsaro a duniya.

“Yaɗa labaran ƙarya ba matsala ce da ta shafi Nijeriya ita kaɗai ba; matsala ce ta duniya baki ɗaya. Mun yaba da ƙoƙarin da UNESCO ke yi wajen yaƙi da wannan matsalar,” inji Idris.

Da yake kira da a haɗa kai a faɗin duniya domin shawo kan wannan matsalar, ministan ya ƙara da cewa yaƙi da baza labaran ƙarya ba yana nufin tauye ’yancin ’yan jarida ne ba.

Ya ce: “Domin al’umma ta kasance ’yantacciya kuma dimokiraɗiyya ta bunƙasa, ’yancin ’yan jarida yana da matuƙar muhimmanci. Amma domin samun wannan ’yanci, dole ne mu ɗauki nauyin da ke tare da shi. Ba za ka yi amfani da ’yancin ka wajen tauye haƙƙin wani ba.”

A nasa ɓangaren, Mista Nelson Papi Kolliesuah, Babban Manajan Ayyuka na Data-Pop Alliance, wato kamfanin da UNESCO ta ɗauka don tantance shirin da Nijeriya ke yi na kafa cibiyar, ya yaba da ƙoƙarin gwamnatin ƙasar.

Ya ce sun zo Nijeriya ne domin tabbatar da cewa an cika sharuɗɗan dukkan kayan aiki, ƙarfin aiki, da tsarin gudanarwa da ake buƙata domin kafa cibiyar.

Ya ƙara da cewa sun gamsu da shirye-shiryen da gwamnatin Nijeriya ta yi, inda ya ce cibiyar ta dace da muradun duniya, tsarin ilimi na Nijeriya, da kuma Muradun Cigaba Masu Ɗorewa na Majalisar Ɗinkin Duniya (MDGs).

Loading

Tags: International Media and Information Literacy InstituteMohammed IdrisNational Open University of Nigeria (NOUN)UNESCO
Previous Post

Mataimakin shugaban MOPPAN reshen Zamfara, Sani Shehu ya riga mu gidan gaskiya

Next Post

Ministan Yaɗa Labarai ya yaba wa BPP kan inganta gaskiya wajen sayen kayayyaki

Related Posts

Yadda CBN ke tallabe da tattalin arzikin Nijeriya, yayin sa farashin ɗanyen mai ke faɗuwar-‘yan-bori a kasuwa
Nijeriya

Yadda CBN ke tallabe da tattalin arzikin Nijeriya, yayin sa farashin ɗanyen mai ke faɗuwar-‘yan-bori a kasuwa

November 7, 2025
Shirin ƙarfafa jari: CBN ya shawarci bankuna marasa ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji
Nijeriya

Shirin ƙarfafa jari: CBN ya shawarci bankuna marasa ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji

November 2, 2025
Bankin CBN ya yunƙuro: Naira ta hana dala numfashi mai ƙarfi a ƙarshen Oktoba
Nijeriya

Bankin CBN ya yunƙuro: Naira ta hana dala numfashi mai ƙarfi a ƙarshen Oktoba

November 2, 2025
Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje
Nijeriya

Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje

October 29, 2025
Tinubu ya yi adalci ga dukkan yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai
Nijeriya

Tinubu ya yi adalci ga dukkan yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai

August 31, 2025
Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar da Sababbin Cibiyoyin Maganin Ciwon Daji

July 24, 2025
Next Post
Ministan Yaɗa Labarai ya yaba wa BPP kan inganta gaskiya wajen sayen kayayyaki

Ministan Yaɗa Labarai ya yaba wa BPP kan inganta gaskiya wajen sayen kayayyaki

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!