• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Tuesday, August 25, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

2023: INEC ta yi wa sassan ta na cikin gida garambuwal

by DAGA WAKILIN MU
April 23, 2021
in Nijeriya
0
2023: INEC ta yi wa sassan ta na cikin gida garambuwal
0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

HUKUMAR Zaɓe Mai Cin Gashin Kan Ta ta Ƙasa (INEC) ta yi wasu sauye-sauye a hedikwatar ta a Sashen Ayyukan Shari’a da Sauraren Koke-koke (LSC &CC) da Sashen Wayar da Kan Masu Zaɓe da Yaɗa Labarai (VEP).

Wannan bayani ya na ƙunshe ne cikin sanarwar da Babban Kwamishina kuma Shugaban Kwamitin Yaɗa Labarai da Wayar da kan Masu Zaɓe na hukumar, Mista Festus Okoye, ya fitar a ranar Laraba.

Haka kuma ya bayyana cewa hukumar ta ƙirƙiro wasu sababbin  ɓangarori guda biyu daga cikin Sashen Ayyukan Shari’a da Sauraren Koke-koke (LSC&CC) na yanzu.

Okoye ya ce sauye-sauyen sun zama dole ne a lokacin da hukumar ke shirin gudanar da muhimman zaɓuɓɓuka na gwamnoni da kuma babban zaɓen 2023.

Ya ce, “Hukumar Zaɓe Mai Cin Gashin Kan Ta ta Ƙasa (INEC) ta yi taro a yau, 22 ga Afrilu 2021, kuma daga cikin abubuwan da aka tattauna har da sauye-sauye da aka yi wa Sashen Shari’a da Sauraren Koke-koke (LSC&CC) da Sashen Wayar da Kan Masu Zaɓe da Yaɗa Labarai (VEP).

“A yayin da hukumar ke shirye-shiryen gudanar da muhimman zaɓuɓɓukan gwamnoni da babban zaɓen 2023, ya zama wajibi a sake yin nazari tare da saisaita wasu daga cikin sassan ta don tabbatar da ingancin aiki da kyakkyawan tsarin tafiyar da ma’aikata da kayan aiki.

“A saboda haka, hukumar ta ƙirƙiro sababbin sassa guda biyu daga cikin Sashen Shari’a da Sauraren Koke-koke (LSC&CC). 

A sabon tsarin, an ƙirƙiri Sashen Ƙararraki (DL&P) da Sashen Rubuta Shari’a (LDCD).”

Kwamishinan ya ƙara da cewa hukumar ta amince da kafa Sashen Ilmantar da Masu Zaɓe, Yaɗa Labarai, Kula da Jinsi da Hulɗa da Ƙungiyoyin Jama’a (VEP) kuma a madadin ta an kafa Sashen Ilmantar da Masu Zaɓe da Yaɗa Labarai (VEP), da kuma Sashen Kula da Jinsi (GID). 

A cewar sa, sauye-sauyen da aka yi Sashen Shari’a da Sauraren Koke-koke (LSC&CC) na gaugawa ne domin hukumar ta duƙufa wajen ƙarfafa ikon ta bisa doka na gurfanar da masu karya dokokin zaɓe a kotu. 

Bugu da ƙari, Okoye ya nanata cewa hukumar ta kuma ƙudiri aniyar sanar da jama’ar Nijeriya dukkan tsare-tsaren ta kuma ta rungumi manyan ƙungiyoyin mata, naƙasassu da sauran jama’ar da ake warewa a harkokin zaɓe. 

A cewar sa, waɗannan sauye-sauye da aka yi ba za su shafi tsari da aikin ofisoshin hukumar na jihohi ba. 

Ya bada tabbacin cewa ofisoshin harkokin shari’a da sasanci na jihohi za su ci gaba da aikin su a ƙarƙashin Shugaban Sashen Ayyukan Shari’a, a yayin da Sashen Kula da Jinsi zai zama a ƙarƙashin Shugaban Sashen Ilmantar da Masu Zaɓe da Yaɗa Labarai. 

Okoye ya nanata cewa sauye-sauyen za su fara aiki ne ba tare da ɓata lokaci ba.

Loading

Previous Post

Tallafin Ramadan: ‘Yan fim sun yaba wa Rarara

Next Post

Daɗi 2: Ɗandugaji ya cika shekara 50, kuma ya zama shugaban ICT a MAKIA

Related Posts

Yadda CBN ke tallabe da tattalin arzikin Nijeriya, yayin sa farashin ɗanyen mai ke faɗuwar-‘yan-bori a kasuwa
Nijeriya

Yadda CBN ke tallabe da tattalin arzikin Nijeriya, yayin sa farashin ɗanyen mai ke faɗuwar-‘yan-bori a kasuwa

November 7, 2025
Shirin ƙarfafa jari: CBN ya shawarci bankuna marasa ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji
Nijeriya

Shirin ƙarfafa jari: CBN ya shawarci bankuna marasa ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji

November 2, 2025
Bankin CBN ya yunƙuro: Naira ta hana dala numfashi mai ƙarfi a ƙarshen Oktoba
Nijeriya

Bankin CBN ya yunƙuro: Naira ta hana dala numfashi mai ƙarfi a ƙarshen Oktoba

November 2, 2025
Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje
Nijeriya

Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje

October 29, 2025
Tinubu ya yi adalci ga dukkan yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai
Nijeriya

Tinubu ya yi adalci ga dukkan yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai

August 31, 2025
Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar da Sababbin Cibiyoyin Maganin Ciwon Daji

July 24, 2025
Next Post
Daɗi 2: Ɗandugaji ya cika shekara 50, kuma ya zama shugaban ICT a MAKIA

Daɗi 2: Ɗandugaji ya cika shekara 50, kuma ya zama shugaban ICT a MAKIA

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!