• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Saturday, June 7, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Ranar ‘yancin ƙasa da kuma wasu ‘yan tsirarun mutane da ke cikin ta

by DAGA LARABI LARABEEN
October 1, 2021
in Tsokaci
0
Shugaba Muhammadu Buhari tare da iyalan sa sun yi shigar fari da tsanwa, su ka ɗau hoto don murnar cikar Nijeriya shekaru 61 da samun mulkin kai... a Fadar Shugaban Ƙasa a yau

Shugaba Muhammadu Buhari tare da iyalan sa sun yi shigar fari da tsanwa, su ka ɗau hoto don murnar cikar Nijeriya shekaru 61 da samun mulkin kai... a Fadar Shugaban Ƙasa a yau

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

RANAR 1 ga Oktoba, 1960 aka ba wa ƙasa ta Nijeriya ‘yanci. Yau 1 ga Oktoba 2021. Shekara 61 kenan. 

A lokacin da na ke rubutun nan, mun kwana uku kenan a jere ba wuta. Na taɓa yin hira da wani ɗan ƙasar Cana ɗan kimanin shekara 34 a duniya a birnin Guangzhou, ya ce min sai da ya girma sannan ya fahimci cewar wutar Nepa ba halitta ba ce ita ma, aikin kimiyya ce. Ya ce da ya ɗauka halitta ce kamar rana da wata da taurari. 

Amma mu a ƙasar mu Nijeriya hatta a Abuja wutar Nepa ba ta tsaya da ƙafafun ta ba, tsawon shekaru 61. 

Mu dawo fagen kiwon lafiya. A wannan rana irin ta yau, a ƙasa ta Nijeriya har yanzu likitoci yajin aiki su ke yi. Gwamnati ta kasa zaunawa ta sasanta da su. 

Batun ilmi ya gurgunce. Kowane lokaci ana cikin yajin aiki. 

Batun tsaro kuwa, wannan ya fi komai lalacewa. Kusan ko’ina a Arewa sai dai hamdala. Wasu mutanen idan abu bai shafi inda su ke kwanciya ba, su ba sa kawo abin a ran su a matsayin matsala. 

Bala’in da mutanen Zamfara, Katsina, Kaduna, Neja, Sakkwato da Kebbi su ke ciki na kidinafas da bandit ya fi na Boko Haram ɗin da aka yi fama da shi a yankin Maiduguri da Yobe. 

Matsalar ruwan sha, ita ma har gobe ana fama da ita.

Matsalar Kayan abinci da tsadar rayuwa. Matsalar noma da kiwo. Matsalar fyaɗe da kashe-kashen aure.

Wasu ‘yan Kannywood su na bikin murnar cikar Nijeriya shekaru 61 da samun mulkin kai… a yau

Fatan mu da burin mu kawai yanzu shi ne Allah ya kawo mana shugabanni nagari, adalai, waɗanda za su gyara ƙasar mu Nijeriya.

Lokacin da na ke rayuwa a ƙasar Sin, wato Cana, garin su Zainab Zhang, na kan yi mamakin wai mutanen da ba su yarda da samuwar Allah s.w.t. ba su ne su ke wannan mulki na adalci a ƙasashen su. Su su ka gina ƙasashen su ta yadda in aka rufe wa ɗan Nijeriya ido ko aka yi masa allurar barci aka kai shi ƙasar idan ya farka aka ce masa ai mutuwa ya yi aka sa shi a Aljanna, zai yi amanna da hakan. 

Mu kuwa a ƙasa ta, an yarda da Allah da ranar Lahira ɗin, amma adalci ya kasa wanzuwa a tsakanin mu. Har talakawan a nan adalci ya yi mana ƙaranci, ba ma iya yi wa kan mu. 

Allah ka raba mu da nadama da ƙasƙanci da bauta a rayuwar mu ta duniya da lahira.

* Larabi Larabeen fitaccen marubuci ne kuma ɗan kasuwa a Kano

Loading

Tags: ChinafataraIndependence DayInsecurity in Nigeriakasar SinKidnappinglantarkiLarabi LarabeenNepaRanar samun 'yanciyunwaZainab Zhang
Previous Post

Babban buri na in ga ranar aure na – Malam Tsalha na ‘Daɗin Kowa’

Next Post

Hotuna: ‘Yan Kannywood sun yi murnar cikar Nijeriya shekaru 61 da samun ‘yanci

Related Posts

Aure Da Saki A Fim: Gangan Ko Gaske?
Tsokaci

Aure Da Saki A Fim: Gangan Ko Gaske?

March 7, 2025
‘Arewa Republic’. Kun gani ba?
Tsokaci

‘Arewa Republic’. Kun gani ba?

February 10, 2025
Rukuni huɗu na masu kallon fim ɗin Hausa
Tsokaci

Rukuni huɗu na masu kallon fim ɗin Hausa

February 7, 2025
Barka Da Zagayowar Ranar Haihuwar Ka Miji Na
Tsokaci

Barka Da Zagayowar Ranar Haihuwar Ka Miji Na

September 1, 2024
Dakta Aliyu U. Tilde
Tsokaci

Arewa: Tsakanin Ilimi Da Sana’a

June 12, 2024
Injiniya Abba Kabir Yusuf (Abba Gida-Gida)
Tsokaci

Shawara ga Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf

June 10, 2024
Next Post
Ali Nuhu, riƙe da tutar Nijeriya kuma sanye da riga mai kalolin tutar, ya yi murnar zagayowar ranar samun 'yancin kai

Hotuna: 'Yan Kannywood sun yi murnar cikar Nijeriya shekaru 61 da samun 'yanci

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!