• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Monday, April 6, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Abin da Umar M. Shareef ya yi mani mai ciwo a harkar waƙa – Abubakar Shinko

by DAGA ABBA MUHAMMAD
September 4, 2022
in Mawaƙa
0
Abubakar Shinko

Abubakar Shinko

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

ABUBAKAR Shinko ya na ɗaya daga cikin matasan mawaƙa masu tasowa a garin Kaduna. Matashin ya ɗauki tsawon lokaci ya na waƙa, amma sai a yanzu ne tauraruwar sa ta fara haskawa.

Mujallar Fim ta tattauna da wannan fasihin, inda ya feɗe mana biri har wutsiya kan ko shi waye da yaushe ya fara waƙa da ko wanene ubangidan shi, da abin da ya sa ya yi waƙar ‘Mutuwar Budurwa’ da kuma wani abu mai ciwo da fitaccen mawaƙi Umar M. Shareef ya yi masa. A sha karatu lafiya.

FIM: Ka faɗa wa masu karatun mu tarihin ka a taƙaice.

ABUBAKAR SHINKO: Da Sunan Allah, Mai Rahama, Mai Jinƙai. Suna na Abubakar Shinko. Ni ɗan garin Kaduna ne.

Na yi karatu na na firamare a Nurul Islam da ke unguwar Rigasa, na kuma yi ƙaramar sakandare na a GSS, duk a nan cikin Rigasa. Daga nan kuma na koma Arewa Model School, inda a nan na kammala karatu na na sakandare. Bayan na gama ne kuma na shiga harkar waƙa.

Shinkon Waƙa

FIM: Wane yare ne kai?

SHINKO: Ni Bahaushe ne. Mahaifin mu ɗan Jihar Sokoto ne, ita kuma mahaifiyar mu ta na ɓangaren Kano da Katsina ne.

FIM: Shekarun ka nawa a duniya?

SHINKO: Zan kimanin shekara 25 a duniya.

FIM: Ya aka yi ka tsinci kan ka a harkar waƙa?

SHINKO: Na tsinci kai na a harkar waƙa dalilin ta na burge ni. Kuma da ma ni mutum ne mai sha’awar isar da saƙo ta hanyar waƙa. Duk wasu abubuwa da ke faruwa na rayuwa zan iya ɗauko shi in sa shi ta waƙa, domin ya fi sauƙin isa wurin jama’a. 

FIM: Ta ina ka fara?

SHINKO: Na fara da waƙoƙin yabo. Tun a lokacin ina Islamiyya, duk ranar Laraba ni ne ke tashi in rera waƙar yabo. Da haka na fara. Sai wani aboki na da ake kiran sa Tijjani ya ce min, “Abubakar, yadda na ga ka iya waƙar yabo, za ka iya irin waƙoƙin Hausa da ake yi.” A lokacin akwai wani kamfanin su, ya ɗauke ni mu ka je wurin, ya ce in kwatanta yi masa waƙa. Da na yi, sai ya ce min gaskiya ta yi daɗi kamar da ma a cikin harkar na ke. A haka dai ya yi ta jan ra’ayi na har ta kai ga yanzu ina cikin harkar dumu-dumu. Yanzu haka na saki album ɗi na mai suna ‘Abokan Juna’, na biyun kuma mai suna ‘Mutuwar Budurwa’ ya na kan hanya.

FIM: A wace shekara ka fara waƙa?

SHINKO: Na fara waƙa a shekarar 2007 zuwa 2008.

FIM: Ka yi waƙoƙi aƙalla za su kai nawa?

SHINKO: Gaskiya ban san adadin su ba.

FIM: Ko za aka iya lissafa mana wasu daga cikin waƙoƙin ka?

SHINKO: Akwai ‘Abokan Juna’, wanda na yi tare da Nura M. Inuwa. Akwai ‘Ameera’, ita ma tare da Nura na yi ta. Akwai ‘Maryama’, wanda na yi tare da Umar M. Shareef. Akwai ‘Bakandamiya’, ‘Sabo Da Juna’, duk tare da Umar na yi su.

FIM: Wace waƙa ce bakandamiyar ka?

SHINKO: ‘Maƙabarta’ ita ce bakandamiya ta. Amma kuma duk waƙoƙi na babu wacce ba na so.

FIM: Me ya sa ka yi waƙar ‘Mutuwar Budurwa’?

SHINKO: Gaskiya labari ne mai tsawo. Mun taso tun mu na yara tare da yarinyar, har ta kai ga mun shaƙu mu na ƙaunar junan mu, har iyayen mu su na mamakin abin. Ko da wani wuri za ta je, sai ta faɗa min. Daga baya sai na fahimci iyayen ta ba su so na da yarinyar; ina ganin canji a idanun su. Daga baya sai su ka ce min za ta yi tafiya, za ta ziyarci dangin baban ta a Kano. Sai na ce mata ya za a yi kenan za ta tafi ta bar ni? Sai ta ce, “Ai sati ɗaya zan yi.” Da ta tafi, sai aka kawo saƙon cewa ita ta rasu, aka kawo gawar ta Kaduna duk a cewa ita ɗin ce ta rasu. Amma ko a lokacin ban yarda da cewa ita ce ta rasu ba, duk da cewa ban duba gawar ba. Labarin na da tsawo, idan ka saurari waƙar za ka fahimci abubuwan da ke ciki. Abu ne wanda ya faru a zahiri. 

FIM: Ka na da ubangida a harkar waƙa?

SHINKO: Gaskiya babu wanda zan ce ga shi shi ne ubangida na. Tun da na fara harkar waƙa da kuɗi na na ke zuwa na biya na yi waƙa na. Ka san da man na ce maka na fara tun daga Islamiyya da waƙoƙin yabo, ka ga ai ba zai ba ni wahala ba. Amma dai a situdiyon Umar M. Shareef na ke waƙoƙi na. Amma ko lokacin da na je, na je masu a matsayin mawaƙi ne. Amma kuma daga baya na koma situdiyon Musa Mairabo. 

FIM: A lokacin da ka ke Shareef Studio, wane irin tallafi shi Umar ɗin ya ba ka?

SHINKO: Gaskiya ya yi min tallafi ta fannin yi min kiɗa mai kyau da kuma yi min aiki mai kyau. Sannan ya na yi min sauƙi wurin biyan kuɗi, domin na kan biya kuɗin waƙa ne kamar guda biyar a lokaci ɗaya.

FIM: Amma bai yi maka ƙoƙarin ya tallafa maka wajen duniya ta san ka kamar yadda duniya ta san shi ba?

SHINKO: Gaskiya bai yi min ba, domin akwai album ɗi na wanda na nemi dama mu yi hoto da shi a saka a bangon album ɗin kafin saki album ɗin a kasuwa, da shi da Nura M. Inuwa, na yi wa Nura magana ya ce in yi wa Umar ɗin magana, da na yi masa magana, sai ya ce min ba zai yiwu na saka hoton su ba, sai dai in saka sunan su. Ya dai nuna min ba zan iya ɗaukan hoto da su ba. A gaskiya ban ji daɗin abin da Umar ya yi min ba.

FIM: A lokacin da ya yi maka wannan abin, ya ka ji a ran ka a matsayin sa na maigidan ka, tunda ka za zauna a ƙasan shi, kuma ka na ba shi girma?

SHINKO: Gaskiya ne! Amma ko da na fara waƙa a Shareef Studio, duk da dai ina zuwa da kuɗi na ne, na je masa matsayin kamar maigida na; ina ba shi girma, da sauran su, amma kuma biyan kuɗi na na ke yi. Amma ka ga duk da wannan ya kasa yi min wannan alfarmar.

FIM: Waɗanne irin nasara ka samu a wannan harka?

SHINKO: Alhamdu lillah, na samu nasarori da dama, tunda ga shi yanzu ina ta ƙara samun masoya. A baya ba a san ni ba, amma ga shi yanzu an san ni. Ina kuma samun saƙonni daga masoya na. Kuma ina samun waƙoƙin biki, na sarauta, suna da sauran su. Waɗannan nasarori ne ba ƙanana ba. 

Cewar Shinko: “Babu wanda zan ce ga shi shi ne ubangida na”

FIM: Ka taɓa yin waƙar fim?

SHINKO: A’a. Ba a taɓa sa waƙa na a fim ba, amma na yi waƙoƙi daban-daban wanda za a iya saka su a fim.

FIM: A ƙarshe, menene saƙon ka ga masoyan ka?

SHINKO: Ina godiya ga masoya na da kuma maƙiya na. Don Allah ku riƙa taya mu da addu’a, kun san yadda yanayin sana’ar ya ke. Ɗan’adam ajizi ne.

Loading

Tags: Abubakar ShinkoKadunamawaƙaNura M. InuwaUmar M. Shareefwaƙa
Previous Post

Mawaƙiya Hajjo Idi Moris ta zama maiɗakin Mika’il

Next Post

Gwamnatin Kano za ta tura ‘yan Kannywood 5 ƙasar Chana domin karatun ilimin fim

Related Posts

Za a yi bikin naɗa Rarara Sarkin Waƙar Ƙasar Hausa a Daura ranar Asabar
Mawaƙa

Za a yi bikin naɗa Rarara Sarkin Waƙar Ƙasar Hausa a Daura ranar Asabar

December 11, 2025
Hotunan Ranar Farko ta taron tunawa da Makaɗa Kassu Zurmi
Mawaƙa

Hotunan Ranar Farko ta taron tunawa da Makaɗa Kassu Zurmi

April 19, 2025
Abin da ya sa nake rubuta littafin rayuwa ta – Ala
Mawaƙa

Abin da ya sa nake rubuta littafin rayuwa ta – Ala

October 28, 2024
Abin da ya sa na koma yin waƙa da kayan kiɗan gargajiya – Aminu Ala
Mawaƙa

Abin da ya sa na koma yin waƙa da kayan kiɗan gargajiya – Aminu Ala

July 16, 2024
Nazarin waƙar ‘Fatima Mai Zogale’ ta Dauda Kahutu Rarara
Mawaƙa

Nazarin waƙar ‘Fatima Mai Zogale’ ta Dauda Kahutu Rarara

May 13, 2024
Waɗansu waliyyai a Nijar da Nijeriya 
Mawaƙa

Waɗansu waliyyai a Nijar da Nijeriya 

December 7, 2023
Next Post
Dama zuwa hagu: Gwamna Ganduje, Alh. Nabraska da Malam Khalid tare da abokan ziyarar a Gidan Gwamnati

Gwamnatin Kano za ta tura 'yan Kannywood 5 ƙasar Chana domin karatun ilimin fim

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!