GWAMNATIN Jihar Kano ta bayyana cewa za ta tura mutum biyar daga masana’antar shirya finafinai ta Kannywood zuwa ƙasar Chana domin su koyo yadda ake shirya fim a zamanance.
Gwamna Abdullahi Umar Ganduje na ya bayyana haka lokacin da dattawan Kannywood su ka kai masa ziyara a Gidan Gwamnati da ke Kano a daren Lahadi, 4 ga Satumba, 2022.
Sun kai ziyarar ne a ci gaba da ƙoƙarin da su ke yi na samar wa da masana’antar su mafita daga matsalolin ta.
Sun je a bisa jagorancin babban mai taimaka wa gwamna a kan Kannywood, Malam Khalid Musa, da kuma mai ba da shawara ga gwamna shawara a kan farfaganda, Alhaji Mustapha Badamasi Nabraska, musamman domin su yi masa godiya saboda muƙaman da ya naɗa ‘yan fim a gwamnatin sa, wanda ya nuna ya na tare da su kamar yadda su ke tare da shi.

Da ya ke jawabi a lokacin zaman nasu da gwamna, Malam Khalid ya bayyana Ganduje a matsayin wanda ya ke kula da harkar matasa da cigaban su, don haka su a matsayin su masu gudanar da sana’ar a Kannywood, su na godiya da kulawar da su ke samu a gwamnatin sa.
Daga nan ya roƙi gwamnan da cewa su na buƙatar ƙarin ilimi a cikin harkar su don su na da masu fasaha da kuma ƙwazon da idan su ka samu damar ƙarin karatu daga waje, to babu shakka masana’antar za ta ci gaba da bunƙasa, wanda kuma yin hakan cigaban Jihar Kano ne da ƙasa baki ɗaya.
A lokacin da ya ke mayar da jawabi, Gwamna Ganduje ya nuna farin cikin sa a game da haɗin kai da ‘yan fim su ke ba gwamnatin sa, kuma ya yi alƙawarin samar da gurbin karatu na mutane biya daga masana’antar finafinan waɗanda za su je ƙasar Chana domin su yi karatun a can.
Ya buƙace su da su je su ga Mataimakin Gwamna, Dakta Nasiru Yusuf Gawuna, wanda shi ne ɗan takarar gwamna a jam’iyyar APC, domin su gabatar masa da ƙudirin.
Ɗaya daga cikin dattawan Kannywood ɗin, wanda tare da shi aka kai ziyarar, Alhaji Sa’idu Isa Gwanja, ya shaida wa mujallar Fim cewa tuni su ka tantance sunayen mutane biyar ɗin da aka nema su ka tura wa gwamnan domin shigar da sunan su.
Ya ce: “Bayan da mu ka dawo, jiya Litinin mu ka tantance sunayen mutane biyar mu ka tura. Kuma a wajen tantancewar mun kalli waɗanda su ke da ƙwarewa da kuma kishin masana’antar finafinai ta Kannywood yadda idan sun yi karatun sun dawo za su taimaki harkar da ma Jihar Kano baki ɗaya.”
![]()







