BABBAR Mataimakiya ga Gwamnan Jihar Kano kan Harkokin Kannywood, Hajiya Aina’u Ade Bello, ta jagoranci rabon tallafin kuɗi ga wasu daga cikin tsofaffin jaruman masana’antar Kannywood.
Tallafin ya fito ne daga ƙungiyar yaƙin neman zaɓen Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, domin wa’adin mulki na biyu, mai taken “AKY Go Again Movement.”
An gudanar da bikin rabon tallafin a jiya Asabar, 22 ga Agusta, 2026, a harabar gidan Rediyon Kano, da misalin ƙarfe 11 na safe, inda manyan ’yan Kannywood da dama suka halarta.
Da take jawabi a wajen taron, Hajiya Aina’u, wadda fitacciyar jarumar Kannywood ce ita ma, ta bayyana cewa manufar tallafin ita ce ƙarfafa tsofaffin jaruman da suka bayar da gagarumar gudunmawa wajen bunƙasa masana’antar Kannywood.

Ta ce yawancin tsofaffin jaruman ba sa samun damar ci gaba da gudanar da ayyukan fim saboda tsufa da kuma matsalolin rashin lafiya da ke addabar su.
Ta yi kira ga waɗanda suka samu tallafin da su yi amfani da kuɗin ta hanyar da ta dace, domin su amfana da shi na tsawon lokaci.
Daga cikin tsofaffin jaruman da suka samu tallafin akwai Ladidi Fagge, Habibu Yaro da Haruna, da sauran tsofaffin ’yan masana’antar.

![]()






