• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Sunday, August 23, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Mutuwar aure na ƙaddara ce – Jaruma Khadija Yobe

by MUKHTAR YAKUBU
August 23, 2026
in Labarai
0
Mutuwar aure na ƙaddara ce – Jaruma Khadija Yobe

Khadija Yobe

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

FITACCIYAR jarumar shirin ‘Izzar So’, Khadija Yobe, ta bayyana cewa mutuwar auren ta wata ƙaddara ce daga Allah.

Ta faɗi haka ne a hirar da ta yi da mujallar Fim.

Kusan shekaru biyar kenan ba a sake jin ɗuriyar  Khadija Yobe ba, wadda aka fi sani da Karima a cikin ‘Izzar So’, tun bayan da ta yi aure.

Jarumar ta auri wani mawaƙin siyasa mai suna Izuddeen, kuma Allah ya albarkaci auren nasu da samun ’ya mace.

Sai dai a ’yan kwanakin nan, wasu hotuna da bidiyoyin da Khadijar ke wallafawa a soshiyal midiya sun fara jawo hankalin masoyan ta, lamarin da ya sa wasu ke tambayar halin da auren ta yake ciki.

A yanzu dai, jarumar ta tabbatar da cewa auren ta ya mutu.

A tattaunawar da ta yi da mujallar Fim ta wayar tarho, Khadija ta ce mutuwar auren nata yana daga cikin jarabawowin rayuwa da Allah ya ƙaddara mata.

“Gaskiya ne aure na ya mutu, kuma yana daga cikin jarabawar da ta same ni. Allah ne ya ƙaddara zan yi aure, sannan daga baya a rabu,” inji ta.

A cewar ta, tun bayan bayyanar labarin rabuwar tasu, tana ci gaba da karɓar kiraye-kiraye da saƙonni daga jama’a da masoyan ta, musamman waɗanda ke bayyana ra’ayoyin su a soshiyal midiya.

Ta ce: “Na daɗe ina karɓar kira daga al’umma da kuma ganin comments game da mutuwar aure na, amma dai mutane su fahimci cewa Allah ne ya ƙaddara hakan.”

Da wakilin mu ya tambaye ta ko tana shirin komawa harkar fim bayan rabuwar auren, jarumar ta ce ba ta yanke shawarar komawa ko kuma ƙin komawa fim ba.

“Ai ina kan ganiya ta na ajiye fim na rungumi aure, don haka ƙaddara ce ta yi sanadin mutuwar auren. Saboda haka ba zan ce zan koma fim ko ba zan koma ba,” inji ta.

Khadija Yobe ta yi kira ga masoyan ta da su ci gaba da yi mata addu’ar samun zaɓin Allah da abin da ya fi alheri a rayuwar ta.

“Ina kira ga masoya na su ci gaba da yi mini addu’ar fatan Allah ya zaɓa mini abin da ya fi alheri a rayuwa ta,” inji ta.

Khadija Yobe na daga cikin fitattun jaruman Kannywood da suka samu gagarumar karɓuwa, musamman sakamakon rawar da ta taka a cikin shirin ‘Izzar So’, inda take fitowa a matsayin Karima.

Khadija Yobe

Loading

Tags: Izzar SoKhadija Yobemutuwar aure
Previous Post

Aina’u Ade ta raba wa tsofaffin jaruman Kannywood tallafin kuɗi

Related Posts

Aina’u Ade ta raba wa tsofaffin jaruman Kannywood tallafin kuɗi
Labarai

Aina’u Ade ta raba wa tsofaffin jaruman Kannywood tallafin kuɗi

August 23, 2026
Ƙungiyar ‘Triple R Kannywood’ ta ziyarci jarumi Tanimu Akawu a asibiti
Labarai

Ƙungiyar ‘Triple R Kannywood’ ta ziyarci jarumi Tanimu Akawu a asibiti

August 23, 2026
Ƙungiyar Triple R ta ba jarumin Kannywood Mustapha Musty tallafin N500,000
Labarai

Ƙungiyar Triple R ta ba jarumin Kannywood Mustapha Musty tallafin N500,000

August 18, 2026
Yadda na gamu da ibtila’in karaya a ƙafa – Jarumi Ɗan’azumi Kamaye
Labarai

Yadda na gamu da ibtila’in karaya a ƙafa – Jarumi Ɗan’azumi Kamaye

August 14, 2026
Tozali TV zai yi bikin Henna Ball da karrama masu ƙwazo da tallafa wa waɗanda suka tsira daga hare-hare a ranar 31 ga Oktoba
Labarai

Tozali TV zai yi bikin Henna Ball da karrama masu ƙwazo da tallafa wa waɗanda suka tsira daga hare-hare a ranar 31 ga Oktoba

August 8, 2026
Tsohuwar matar Adam Zango, Maimuna Musa, ta tabbatar da dalilin rabuwar auren su
Labarai

Tsohuwar matar Adam Zango, Maimuna Musa, ta tabbatar da dalilin rabuwar auren su

August 2, 2026
  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!