• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Friday, July 18, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Abin da ya sa na ke ciyar da yara da azumi – Daso

by DAGA MUKHTAR YAKUBU
April 8, 2023
in Labarai
0
Hajiya Saratu ta na miƙa abinci ga wasu yara a gidan ta

Hajiya Saratu ta na miƙa abinci ga wasu yara a gidan ta

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

KAMAR yadda ta saba yi a kowace shekara, a bana ma jarumar Kannywood Saratu Gidado (Daso) ta ci gaba da rabon abincin buɗa-baki ga yara a gidan ta.

A kullum Hajiya Saratu na ciyar da yara da ke cika a gidan ta da ke Unguwar Chiranci a cikin Birnin Kano.

A wajen rabon abincin, kamar yadda wakilin mujallar Fim ya gani a jiya Juma’a, ana raba dafaffiyar shinkafa da taliya da doya da naman kaji da na shanu da kuma kayan marmari.

Da mujallar Fim ta tambaye ta dalilin wannan ciyarwar da ta ke yi da azumi, sai Daso ta ce: “To, ita wannan ciyarwar da man ina yin ta duk ranar Juma’a. Na kan tara yara na raba musu abinci sadaka, amma da azumi kullum na ke fadawa na raba, kuma haka na ke yi duk shekara.”

A game da maganar da ake yi na cewar ciyarwar da ta ke yi iya yara ne kuwa, cewa ta yi, “To gaskiya ni ciyarwar da na fi mayar da hankali a kan ta ita ce ta marayu da kuma almajirai, don haka aka fi ganin yara a wajen rabon abincin da na ke yi. 

Dandazon yara masu karɓar abincin buɗa-baki a wajen Daso

“Su marayu da almajirai su ne su ka fi zama abin tausayi, shi ya sa na fi mayar da hankali a kan su. Amma su ma manyan mu na raba musu, don mu na ɗaukar kayan abinci mu shiga ƙauyuka domin raba wa mabuƙata.”

Da mu ka tambaye ta ko akwai bambanci tsakanin wannan shekarar da bara, sai ta ce, “Gaskiya akwai bambanci, domin a shekarar da ta gabata mun fi samun tallafi daga wajen mutane da su ke bayar da gudunmawar kayan abincin da mu ke rabawa, amma a bana ko don yanayin da ake ciki ne ya sa ba mu samu ba. Wannan shekarar gaskiya akwai ƙarancin abubuwan da mu ke samu na gudunmawa don rabawa ga jama’a. Amma dai har yanzu ƙofar mu a buɗe ta ke ga duk wanda ya ke son ya bayar da tasa gudunmawar domin ciyar da masu buƙatar da mu ke da su, don su na da yawa a cikin al’umma. Fatan mu dai Allah ya haɗa mu a ladar.”

Loading

Tags: ciyarwar azumimarayuRamadanSaratu Giɗaɗo Dasotallafi Chiranciyara
Previous Post

Yadda rikicin kuɗi ya farraƙa sabuwar ƙungiyar mawaƙa mata – Fati Kawo

Next Post

Kamal mai zane ya shawarci ‘yan ƙungiyar mawaƙa mata da su tuntuɓi Iyan-Tama

Related Posts

Hukumar Shari’a da Hukumar Tace Finafinai za su haɗa gwiwa don tsaftace tarbiyya a Kano
Labarai

Hukumar Shari’a da Hukumar Tace Finafinai za su haɗa gwiwa don tsaftace tarbiyya a Kano

July 11, 2025
Labarai

Jarumin Kannywood, Baba Ƙarami ya yi magana kan ganin sa da aka yi kan keken guragu 

July 10, 2025
Tsohuwar jarumar Kannywood, Halisa tana neman addu’a
Labarai

Tsohuwar jarumar Kannywood, Halisa tana neman addu’a

July 9, 2025
Mawaƙin Manzon Allah, Abdullahi Ɗan Gano ya rasu
Labarai

Mawaƙin Manzon Allah, Abdullahi Ɗan Gano ya rasu

July 7, 2025
MOPPAN ta yi wa al’ummar Kano ta’aziyyar Aminu Ɗantata 
Labarai

MOPPAN ta yi wa al’ummar Kano ta’aziyyar Aminu Ɗantata 

June 29, 2025
Ƙungiyoyin harkar fim, KAFIGAN da MOPPAN, sun yi wa Rahama Sadau ta’aziyyar rasuwar mahaifin ta
Labarai

Ƙungiyoyin harkar fim, KAFIGAN da MOPPAN, sun yi wa Rahama Sadau ta’aziyyar rasuwar mahaifin ta

June 23, 2025
Next Post
Kamal Y. Iyan-Tama

Kamal mai zane ya shawarci 'yan ƙungiyar mawaƙa mata da su tuntuɓi Iyan-Tama

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!