• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Saturday, June 7, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Agajin marasa galihu: Ma’aikatar Jinƙai ta fara tantance sunayen waɗanda hare-haren ‘yan ta’adda ya shafa a Jihar Katsina

by DAGA WAKILIN MU
December 24, 2022
in Nijeriya
0
Hajiya Sadiya Umar Farouq

Hajiya Sadiya Umar Farouq

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

GWAMNATIN Tarayya ta fara tattara sunayen waɗanda hare-haren ‘yan ta’adda ya shafa a wasu ƙananan hukumomi na Jihar Katsina.

Aikin tantance sunayen, wanda ake gudanarwa a ƙarƙashin Ma’aikatar Ayyukan Jinƙai, Agaji da Inganta Rayuwa wadda Hajiya Sadiya Farouq ce minista, zai ɗauki sunayen ne daga ƙananan hukumomi 11 domin su shiga cikin tsarin masu cin gajiyar shirye-shiryen da ma’aikatar ke samar wa marasa galihu a faɗin ƙasar nan.

Jagorar tawagar da ma’aikatar ta tura Katsina domin wayar da kan jama’a dangane da shirin, Hajiya Nadia Muhammad, ita ce ta bayyana haka.

Hajiya Nadia ta ce: ”Waɗanda hare-haren ‘yan bindiga ya shafa su na cikin wani halin da su ke matuƙar buƙatar samun tagomashin canjin rayuwa.”

Daga cikin tsare-tsaren da za a saka sunayen waɗanda za a tantance ɗin har da shirin bayar da tallafin kuɗaɗe ga marasa galihu, shirin bayar da jarin tallafawa domin a yi ƙananan sana’o’i, shirin N-Power, shirin ciyar da ɗalibai da sauran su.

Da ta ke jawabi, Madam Funke Olatunji, wadda ta wakilci Shugabar Sashen Ayyukan Musamman a ma’aikatar, wato Nadia Muhammad, ta ce matsalar tsaro ta kawo cikas sosai wajen kasa kai kayan agaji da gudanar da ayyukan jinƙai a wasu yankunan karkarar da ‘yan bindiga su ka addabi jama’a da dama.

Ta ce: “Dalilin haka ne wannan ma’aikata ta fito da shirin tantance sunayen domin su riƙa cin moriyar ayyukan wannan ma’aikata kai-tsaye.” 

Ta gode wa gwamnatin Jihar Katsina dangane da ƙoƙarin da ta ke kan yi wa waɗanda hare-haren ‘yan bingida ya shafa.

Wasu waɗanda hare-haren ‘yan ta’addar ya shafa daga ƙananan hukumomin Jibiya, Batsari da Kurfi, sun shaida wa jami’an shirin cewa su na buƙatar muhalli.

Loading

Tags: agajiFunke Olatunjihare-hareJihar KatsinaN-PowerNadia Muhammadrashin tsaroSadiya Umar Farouq
Previous Post

An ɗaura: Jarumin Kannywood Yusuf Saseen ya zama angon Amina

Next Post

Kannywood: Auren SS Danko da Nusaiba ya tabbata

Related Posts

Gwamnatin Tarayya za ta tallafa wa yekuwar rigakafin cutar ƙyandar Jamus
Nijeriya

Gwamnatin Tarayya za ta tallafa wa yekuwar rigakafin cutar ƙyandar Jamus

June 4, 2025
Tinubu ya tura wakilai zuwa Neja kan ambaliyar Mokwa da ta halaka sama da mutum 150
Nijeriya

Tinubu ya tura wakilai zuwa Neja kan ambaliyar Mokwa da ta halaka sama da mutum 150

May 31, 2025
Gwamnatin Nijeriya ta goyi bayan amfani da Ƙirƙirarrar Basira cikin ɗa’a a aikin jarida – Idris
Nijeriya

Gwamnatin Tarayya ta yi ta’aziyyar mutanen da suka rasu a ambaliyar garin Mokwa

May 30, 2025
Babu wasu masu juya Tinubu ta bayan fage – Idris
Nijeriya

Babu wasu masu juya Tinubu ta bayan fage – Idris

May 25, 2025
Shirye-shiryen Shugaba Tinubu Suna Buɗe Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya – Idris
Nijeriya

Shirye-shiryen Shugaba Tinubu Suna Buɗe Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya – Idris

May 20, 2025
Idris ya ƙaryata ji-ta-ji-tar an mayar da taron bayanin ministoci zuwa London
Nijeriya

Idris ya ƙaryata ji-ta-ji-tar an mayar da taron bayanin ministoci zuwa London

May 16, 2025
Next Post
Ango Ibrahim SS Danko (a dana) tare da mawaƙi Auta MG Boy a wurin ɗaurin auren

Kannywood: Auren SS Danko da Nusaiba ya tabbata

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!