A YAU da yamma aka fara shagalin auren ‘yar jaruma Hajiya Asma’u Sani, wato A’isha Ibrahim Yusuf, wadda za a ɗaura wa aure a jibi Juma’a.
Bikin na yau an yi masa taken Ranar Ƙauyawa, inda aka yi shiga irin ta ‘yan matan ƙauye.


Kamar yadda al’adar bikin take, ƙawayen amarya da yayye da ƙannen amarya ne suke taruwa domin yin gaɗa da sauran waƙoƙi irin na gargajiya.

Su kan su ƙawayen uwar amarya ‘yan fim ba a bar su a baya ba domin kuwa jaruman fim da dama sun halarci taron wanda aka gudanar a Gidan Danhausa da ke cikin Nassarawa GRA a Kano.

Jaruman Kannywood da suka halarta sun haɗa da Halisa Muhammad, Yahanasu Sani, Maijidda Abbas, Jamila Gamdare, Ummi Gombe, Hadizan Saima, Bilkin AK, Maryam CTV, Fati Gwammaja, da sauran su.
An dai yi taron an tashi lafiya.
Sai kuma idan Allah ya kai mu gobe za a shiga rana ta biyu ta bikin.