• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Wednesday, June 4, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Attah Dabai: Ba rabo da gwani ba…

by DAGA IBRAHIM SHEME
November 2, 2021
in Tsokaci
0
Alhaji Attah Dabai a bangon sashen Bahaushiya na cikin mujallar Fim ta Janairu, 2014

Alhaji Attah Dabai a bangon sashen Bahaushiya na cikin mujallar Fim ta Janairu, 2014

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

ALLAHU Akbar! Rai baƙon duniya! Sai ɗazu na samu labarin rasuwar shahararren makaɗi kuma mawaƙin Hausa ɗin nan Alhaji Attah Dabai – kwana huɗu bayan rasuwar sa. An ce ya rasu a ranar Juma’a da ta gabata a garin Dabai da ke Ƙaramar Hukumar Ɗanja a Jihar Katsina. An ce ya haura shekara ɗari a duniya.

Dattijon arziki ne, Alhaji Attah Dabai.

A wannan hoton, za a gan ni ina tattaunawa da shi a gidan shi a cikin watan Nuwamba, 2013 (yanzu shekara takwas cur). Editan Mujallar Fim a lokacin, Aliyu A. Gora II, wanda tare mu ka je Dabai daga Kaduna, shi ya ɗauki hoton. A ɗaya hoton kuma Alhaji Attah ɗin ne a bangon Bahaushiya (wani sashe a cikin mujallar Fim), a fitowar ta ta Janairu 2014 lokacin da aka wallafa waccan hirar da na yi da shi. Ni na ɗauki hoton.

Ina tattaunawa da Attah Dabai a zauren gidan shi a cikin Nuwamba 2013

Gani na na ƙarshe da shi (tare da ‘ya’yan sa, su Alhaji Saleh Dabai) ya faru ne a cikin Afrilu 2018 a garin Abeokuta, Jihar Ogun, a wajen bikin kaɗe-kaɗen gargajiya na nahiyar Afrika (African Drum Festival). Su sun je ne daga Katsina a matsayin wakilan jihar a bikin, ni kuma na je daga Legas a bisa gayyatar masu shirya bikin (su Wole Soyinka) saboda wata alaƙa ta da su mashirya bikin.

Na san cewa da yawa matasan yanzu ba su san  waƙoƙin marigayi Attah Dabai ba kamar yadda su ka san waƙoƙin Shata ko Ɗanƙwairo. To ai kuwa ya yi waƙoƙi da dama, inda har ya samar da wasu mawaƙan, kamar misali Alhaji Shehu Ajilo Ɗanguziri.

Alhaji Saleh Dabai a wajen Bikin Kaɗe-kaɗen Gargajiya na Afrika da aka yi a Abeokuta a cikin Afrilu 2018.

Attah Dabai ya ciri tuta ne a fagen kiɗan dandali wanda ake kira “saran marke”, inda su ke kaɗa wata ƙaramar ganga. A wannan fage, duk ƙasar Hausa babu kamar Attah Dabai da ‘ya’yan sa. Idan ka ga wasan sa, musamman lokacin da ya ke matashi (ina da bidiyon hakan), to ba za ka taɓa mantawa da salon kiɗa da rawar ba, domin har daga kwance ya na kiɗa! Zarrar da su ka yi a fagen ya sanya a ko yaushe ake shigar da su bukukuwan al’adun gargajiya. 

Hasali ma dai, babu makaɗin Hausa da ya kai Attah Dabai yawo ko ziyartar ƙasashen duniya. E, har Shata! Daga shi, sai Alhaji Adamu Ɗanmaraya Jos. Shi ne ma Sarkin Kiɗan Sarkin Katsina.

Shata ubangidan sa ne. Shata ne ya biya masa kujerar aikin Makka ɗaya da ya je, bayan ya yi wa Shatan kiɗa a Bakori lokacin da ya auri wata mace.

Marigayi Attah Dabai da ‘ya’yan sa su na wasa a gaban Hakimin Bakori a wajen wani babban taro da aka yi a Bakori, Jihar Katsina

Hausawa sun ce ba rabo da gwani ba, kafin a samu gwani daga ne! Labarin Alhaji Attah Dabai ya na da tsawo, sai dai a taƙaita. Ina yi wa iyalin shi ta’aziyya. Allah ya jiƙan Baba, ya kyautata makwancin sa, amin summa amin.

Loading

Tags: Adamu Danmaraya JosAfrican Drum Festivalaladun gargajiyaAliyu A. Gora IIAttah DabaiBahaushiyagangaMamman ShataMujallar FimmutuwaSaleh Dabaisaran markeShehu Ajilo Danguziri
Previous Post

INEC ta yi wa masu zaɓe 30,449 rajista a Filato

Next Post

Cewar Farfesa Yakubu: INEC ta shirya wa zaɓen gwamnan Anambra na ranar Asabar

Related Posts

Aure Da Saki A Fim: Gangan Ko Gaske?
Tsokaci

Aure Da Saki A Fim: Gangan Ko Gaske?

March 7, 2025
‘Arewa Republic’. Kun gani ba?
Tsokaci

‘Arewa Republic’. Kun gani ba?

February 10, 2025
Rukuni huɗu na masu kallon fim ɗin Hausa
Tsokaci

Rukuni huɗu na masu kallon fim ɗin Hausa

February 7, 2025
Barka Da Zagayowar Ranar Haihuwar Ka Miji Na
Tsokaci

Barka Da Zagayowar Ranar Haihuwar Ka Miji Na

September 1, 2024
Dakta Aliyu U. Tilde
Tsokaci

Arewa: Tsakanin Ilimi Da Sana’a

June 12, 2024
Injiniya Abba Kabir Yusuf (Abba Gida-Gida)
Tsokaci

Shawara ga Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf

June 10, 2024
Next Post
Farfesa Mahood Yakubu

Cewar Farfesa Yakubu: INEC ta shirya wa zaɓen gwamnan Anambra na ranar Asabar

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!