• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Thursday, June 5, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Ba mu buƙatar amincewar Sanusi kan tsare-tsaren mu na tattalin arziki, inji Ministan Yaɗa Labarai

by WAKILIN MU
January 16, 2025
in Nijeriya
0
Gwamnatin Tarayya ta jajanta wa iyalan waɗanda suka rasu a turereniya, ta ba da shawara kan bukukuwan Kirsimeti 

Alhaji Mohammed Idris

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

GWAMNATIN Tarayya ta mayar da martani kan kalaman Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II, kan tsare-tsaren gyaran tattalin arziki da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu take aiwatarwa, tana mai bayyana su a matsayin marasa amfani kuma na son rai.

A wata sanarwa da Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya fitar a ranar Laraba, ya bayyana cewa Nijeriya tana cikin wani muhimmin mataki da ke buƙatar matakan da suka dace da kuma ƙarfin hali domin magance manyan matsalolin tattalin arziki.

Ministan ya nuna jin daɗin sa kan yadda Sanusi ya amince da wasu tsare-tsaren gwamnati, amma ya nuna damuwa kan yadda Sarkin ya bayyana cewa ba zai goyi bayan gwamnati ba saboda wasu dalilai na son rai.

Ya ce: “Abin takaici ne yadda shugaba daga masarauta mai daraja da son tsare gaskiya da adalci zai fito fili ya ce ba zai faɗi gaskiya ba saboda dalilan kan sa.”

Ya jaddada cewa gyare-gyaren da gwamnatin ta yi, kamar daidaita farashin dala da kuma cire tallafin man fetur, sun zama dole domin magance shekaru na gazawa wajen gudanar da tattalin arzikin ƙasa.

Idris ya bayyana cewa an fara ganin sakamakon waɗannan matakai ƙarara, wanda ya haɗa da ƙaruwar ajiyar kuɗaɗen waje, ƙaruwar ƙwarin gwiwar masu zuba hannun jari, da rage yawan bashin da ake biya.

Ministan ya bayyana cewa sukar da sarkin ya yi ba ta dace ba, musamman ganin cewa ya taɓa goyon bayan irin waɗannan matakan a baya. Ya yi kira ga Sanusi da ya fifita cigaban ƙasa a kan son rai.

Ya ce: “Gyaran Nijeriya tana buƙatar haɗin kai, mayar da hankali, da sadaukarwa daga dukkan masu ruwa da tsaki.
“Ya kamata shugabanni su zama jagororin cimma muradun cigaban ƙasa, ba masu tauye amanar jama’a ba.”

Idris ya sake tabbatar da aniyar gwamnatin ta bunƙasa tattalin arziki mai ɗorewa, tare da yin kira ga ’yan Nijeriya su ba da haɗin kai domin samun nasarar waɗannan tsare-tsare.

Ministan ya jaddada cewa gwamnati a shirye take don tattaunawa mai amfani da dukkan masu ruwa da tsaki, tare da tabbatar da cewa tana kan hanyar cika burin samar da ƙasa mai inganci ga kowa.

Loading

Tags: Mohammed IdrisSarkin Kano Muhammadu Sanusi IItattalin arziki
Previous Post

Majalisar Dattawa ta yaba wa Ministan Yaɗa Labarai kan nasarori, ta nemi ƙarin kasafin kuɗi na musamman ga ma’aikatar

Next Post

Tinubu ya himmatu wajen kammala hanyar Abuja zuwa Kano cikin watanni 14, cewar Ministan Yaɗa Labarai

Related Posts

Gwamnatin Tarayya za ta tallafa wa yekuwar rigakafin cutar ƙyandar Jamus
Nijeriya

Gwamnatin Tarayya za ta tallafa wa yekuwar rigakafin cutar ƙyandar Jamus

June 4, 2025
Tinubu ya tura wakilai zuwa Neja kan ambaliyar Mokwa da ta halaka sama da mutum 150
Nijeriya

Tinubu ya tura wakilai zuwa Neja kan ambaliyar Mokwa da ta halaka sama da mutum 150

May 31, 2025
Gwamnatin Nijeriya ta goyi bayan amfani da Ƙirƙirarrar Basira cikin ɗa’a a aikin jarida – Idris
Nijeriya

Gwamnatin Tarayya ta yi ta’aziyyar mutanen da suka rasu a ambaliyar garin Mokwa

May 30, 2025
Babu wasu masu juya Tinubu ta bayan fage – Idris
Nijeriya

Babu wasu masu juya Tinubu ta bayan fage – Idris

May 25, 2025
Shirye-shiryen Shugaba Tinubu Suna Buɗe Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya – Idris
Nijeriya

Shirye-shiryen Shugaba Tinubu Suna Buɗe Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya – Idris

May 20, 2025
Idris ya ƙaryata ji-ta-ji-tar an mayar da taron bayanin ministoci zuwa London
Nijeriya

Idris ya ƙaryata ji-ta-ji-tar an mayar da taron bayanin ministoci zuwa London

May 16, 2025
Next Post
Tinubu ya himmatu wajen kammala hanyar Abuja zuwa Kano cikin watanni 14, cewar Ministan Yaɗa Labarai

Tinubu ya himmatu wajen kammala hanyar Abuja zuwa Kano cikin watanni 14, cewar Ministan Yaɗa Labarai

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!