• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Monday, April 6, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Batun matar aure: Kotu ta ce a kamo mata Rarara

by DAGA MUHAMMAD LAWAN RANO
December 22, 2020
in Uncategorized
0
Dauda Kahutu (Rarara)

Dauda Kahutu (Rarara)

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

WATA kotu a Kano a yau ta bada umarnin gaggawa a kamo mata fitaccen mawaƙi Dauda Kahutu (Rarara) a kan zargin raina kotu.  Da ya ke yanke hukuncin, Mai Shari’a Khalid Ibrahim Sarki Yola ya bada wannan umarnin ne saboda bijire wa umarnin kotun ta shari’ar Musulunci da Rarara ya yi kan ya bayyana a gaban kotun domin ya kare kan sa kan wani zargi da ake masa. 

Idan kun tuna, mujallar Fim ta ba ku labarin yadda wani mutum ya yi barazanar zai maka Rarara a kotu kan tuhumar sa da saka matar sa Maryam a cikin bidiyon wata waƙar siyasa da ya yi a Katsina mai suna ‘Jiha Ta’ da kuma ɓoye matar. An tsara waƙar ne don a nuna alhini kan matsalar rashin tsaro da ke faruwa a Jihar Katsina, kuma Ali Nuhu da Isa Alolo ne su ka bayar da umarni a wajen shirya bidiyon ta.

Maryam na daga cikin ‘yan fim da su ka fito a bidiyon waƙar.

Mijin ta ya yi iƙirarin cewa auren su da ita dududu bai wuce watanni biyar ba, kuma ya sha alwashin maka Rarara a kotu domin ya saka matar sa a fim ba tare da izinin sa ba.

Daga nan ya cika alƙawarin da ya yi na maka mawaƙin a kotu a ranar 1 ga Disamba.

Bisa wannan tuhumar ce kotu ta aike wa da mawaƙin sammaci kan ya bayyana a gaban alƙali a yau Talata, 22 ga wata.

Rarara dai bai je kotun a yau ba.
Sai dai a bayanin da ta saki ta hanyar bidiyo a Instagram, Maryam ta wanke Rarara daga zargin da ake yi masa, ta na faɗin ita yanzu ba ta da aure. Ta ce: “Babu ruwan Rarara, kawai tsohon miji na, ya yi haka ne domin ya ɓata mai suna ya kuma zubar mai da mutuncin sa.” A bayanin nata, sabuwar jarumar ta bayyana cewa shi mijin nata ya na so ne su koma su ci gaba da zaman aure, ta ce, “ni kuma na ce ba zan koma ba.” Ta ce, “Saboda irin sakin wulaƙancin da ya min ne ba zai iya zuwa ya haɗa idanu da iyaye na ba, ya fuskance su ya ce zai dawo da ni; to shi ne ya zagayo ta wannan hanyar don ya zubar min da mutunci ya kuma zubar wa da Rarara da mutunci.” Maryam ta ƙara da cewa ita ba ma Rarara ne ya ɗauke ta ya saka ta a bidiyon waƙar tasa ba. 

“Furodusa ne ya ɗauke ni kuma shi ma ba shi ya ɗauke ni ba, ƙawa ta ya ɗauka, shi ne ta ɗauke ni mu ka je. “Kuma da na je sai da na kira mahaifiya ta na haɗa su su kai magana, kuma aka ce in an gama za a kai ni a tantance ni.  

“Amma shi ne ya zagayo daga baya ya na cewa ina da aure. To ni ba ni da aure! “Don haka shi Rarara bai ma san ni ba, bai ma taɓa gani na ba sai ranar da za a ɗauki bidiyon, har yake tambaya wace ce waccan da aka ce an zo da ita.”

Loading

Previous Post

An ɗaura: Sa’a Vocal ta zama amaryar Haiwatu

Next Post

Hisbah da masu gidajen kallo sun samu cimma matsaya a Kano

Related Posts

Rasuwar dattijon Kannywood, Nura Shareef, ta girgiza ‘yan fim
Labarai

Rasuwar dattijon Kannywood, Nura Shareef, ta girgiza ‘yan fim

February 22, 2026
Daraktar fim ta ƙi karɓar awad saboda kisan gillar da Isra’ila take yi a Gaza
Labarai

Daraktar fim ta ƙi karɓar awad saboda kisan gillar da Isra’ila take yi a Gaza

February 21, 2026
Fitaccen furodusa Kunle Afolayan ya yi haɗin gwiwa da Jamhuriyar Benin kan shirya finafinai
Labarai

Fitaccen furodusa Kunle Afolayan ya yi haɗin gwiwa da Jamhuriyar Benin kan shirya finafinai

February 19, 2026
An naɗa Farfesa Tengya matsayin sabon shugaban Cibiyar Koyon Finafinai ta Ƙasa
Labarai

An naɗa Farfesa Tengya matsayin sabon shugaban Cibiyar Koyon Finafinai ta Ƙasa

February 15, 2026
Alƙali ya ci Samha Inuwa tara ko ta je kurkuku wata 6
Labarai

Alƙali ya ci Samha Inuwa tara ko ta je kurkuku wata 6

February 13, 2026
Hukumar EFCC ta kama jarumar Kannywood, Samha Inuwa, saboda goge majina da takardun naira
Labarai

Hukumar EFCC ta kama jarumar Kannywood, Samha Inuwa, saboda goge majina da takardun naira

February 3, 2026
Next Post
Malam Haruna Ibn Sina, Babban Kwamandan Hukumar Hisbah ta Jihar Kano

Hisbah da masu gidajen kallo sun samu cimma matsaya a Kano

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!