SAFNA Lawan, wadda jaruma ce a Kannywood, ta nuna takaici a game da rashin samun dama da ƙananan jarumai su ke yi a cikin masana’antar, ba kamar yadda ake yi a Hollywood da Bollywood ba.
A a lokacin tattaunawar ta da mujallar Fim, jarumar ta ce, “Yanzu kamar a Indiya ne, idan ƙaramar jaruma ta shigo za su yi yadda za su yi ne su sa duniya ta san ta har a yi alfahari da ita. To a nan ne za a gane ƙwarewar ta.
“Don haka abin da ya kamata a riƙa yi wa ƙananan jarumai idan sun shigo Kannywood a riƙa ba su sin ɗaya biyu a cikin fim, ko da kuwa kurman sin ne. A nan za a ga ƙwarewar sa har a ba shi babban fim.
“To a gaskiya mu na da ƙarancin wannan ga kuma jarumai mata ɗin. Mun yi yawa, don haka ya kamata a duba wannan matsalar.”

Dangane da nasarorin da ta samu dangane da harkar fim kuwa, Safna ta ce, “A gaskiya na samu nasarori da yawa domin na shiga manyan finafinai kamar ‘Laure’, ‘Izzar So’, ‘Ina Da Buri’, sannan na samu damar shiga fim ɗin ‘Sarah’.”
Safna ta ce tun ta na ƙarama harkar fim ke burge ta. A cewar ta, “Da man tun ina ƙarama na ke da burin shiga harkar fim, kuma sai na samu kai na a cikin maraici inda na tashi a cikin maraicin rashin uwa. Hakan sai ya ƙarfafa mini gwiwa, domin ina son na faɗakar da jama’a kuma a yanzu ga shi na samu dama.
“Don haka a yanzu babban burin da na ke da shi na ga na samu zama babbar jaruma da duniya ta san da ita. Don haka ina fatan Allah ya cika mini burin da na ke da shi.”
Dangane da daɗewar da ta yi a cikin harkar fim kuwa cewa ta yi, “To gaskiya a yanzu zan kai wajen shekaru takwas, amma dai a baya da na fara na kowa gida Kaduna na ci gaba da zama, sai daga baya na dawo. Kuma yanzu da dawowa ta ban fi shekara ɗaya ba.
“Sai dai a dawowar da na yi ina ganin alamun nasara sosai, don yanzu ina samun aiki, ana kira na duk wani babban aiki da za a yi. Wannan ya sa na ke ganin nan da ɗan lokaci kaɗan da yardar Allah zan cimma buri na na zama babbar jaruma.”