• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Friday, June 6, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Cewar Hannatu Bashir: Abin takaici ne yadda mazan Kannywood irin su Adam Zango suke ɓata sunan matan industiri

Wallahi ni ban fi ƙarfin iyaye na ba, inji ta

by ABBA MUHAMMAD
February 15, 2024
in Labarai
0
Cewar Hannatu Bashir: Abin takaici ne yadda mazan Kannywood irin su Adam Zango suke ɓata sunan matan industiri

Hajiya Hannatu Bashir ta ce ba yi wa mata adalci

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

JARUMA kuma furodusa a Kannywood, Hajiya Hannatu Bashir, ta mayar da kakkausan martani ga Adam A. Zango kan iƙirarin sa na cewa matan Kannywood ba da son ran iyayen su su ke shigowa fim ba.

Jarumin kuma mawaƙi ya faɗa a wata hira da ya yi da BBC Hausa a makon jiya cewa duk yarinyar da aka ga tana fim, to ta fi ƙarfin iyayen ta ne.

A martanin da ta yi masa a TikTok, kashi na 1 zuwa na 5, Hannatu ta ce: “Ina da ɗan wani tsokaci ne, mutanen mu abin da zan iya ce mana kullum shi ne, kullum mu na hawa kyamara, sannan kullum mu na mu’amala da kyamara, sannan kullum a cikin intabiyu mu ke. Amma wani sa’in furucin da mu ke yi akwai kurakurai da yawa a ciki.

“Mu riƙa sanin me za mu faɗa saboda mu riƙa yi wa junan mu adalci baki ɗaya. Mutum ɗaya idan ya yi intabiyu ya faɗi wata kalmar, gaba ɗaya sai ta ɓata kowa, ta ja wa kowa baƙin jini ko zagi ko baƙar magana.”

Hannatu, wadda ke zaune a cikin mota a bidiyoyin da ta wallafa, ta ci gaba da cewa, “Na ji wata intabiyu, wani na cewa menene, matan Kannywood da yawa da su ke shigowa sun fi ƙarfin iyayen su, iyayen su ba su isa da su ba.

“Wannan kuskure ne a cikin maganar. Ya kamata mu riƙa sanin me za mu rinƙa faɗa saboda mu riƙa yi wa junan mu adalci.

“Wallahi ban fi ƙarfin iyaye na ba! Har yanzu iyaye su su ke faɗa min in ji, abin da su ke so shi na ke yi. Babu wata mace da za a ce ta fi ƙarfin iyayen ta ne ta zo Kannywood, a Kannywood wa zai faɗa mata ta ji. Wannan ba furuci ba ne.

“Sannan kuma da ake cewa ta fi ƙarfin gidan su ne ta shigo fim, idan aka yi wannan furucin, za a ce fim ba sana’a ba ce? In ba sana’a ba ce, shi wanda ya ke maganar me ya sa ya ke yi in ba sana’a ba ce?

“So, don Allah mu rinƙa yi wa junan mu adalci.

“Kuma mu mata kullum mu ku ke ja wa baƙin jini, ku riƙa ɗauko wasu maganganu wanda ba kwa yi mana adalci ku na ɗorawa a kan mu, kuma duniya ta riƙa kallon mu da shi ta na zagin mu da shi. Sunan mu mata fa; mu na so mu haihu, za mu yi aure, za mu haifi ‘ya’ya, ku na bar wa ‘ya’yan mu wani abin da za a ce ga abin da iyayen ku su ka yi, tunda wani ne ya ke faɗa ba mu ba ne mu ke yi.

“Ta ina za ta fito a ce ta fi ƙarfin iyayen ta? Ta ina za ka ce wai mace ta baro gidan su ta shigo sana’ar fim wai ta fi ƙarfin iyayen ta, to wa zai faɗa mata ta ji? Saboda shi fim ɗin ba sana’a ba ne?

“Har ga Allah, tun da na shiga harkar fim, sana’a na ɗauke ta kuma sana’a na ke yi.”

Hannatu Bashir (Hanan) cikin bidiyon martanin da ta wallafa a Tiktok 

Haka kuma jarumar ta ce, “So, sannan ni don kullum ana cewa duk macen da ta shigo harkar fim ba da son ran iyayen ta ba. Tambaya ta a nan ita ce, ƙasar ita mace idan aka ta shigo harkar fim ba da son ran iyayen ta ba, shi fim ɗin ba sana’a ba ne? Ita ce kawai tambaya ta, amsar da na ke so kenan.”

“Idan ba sana’a ba ne, shi wanda ya ke maganar bai ma kamata ya yi ta ba tunda ba sana’a ba ne. Duk abin da ka san ba sana’a ba ne, bai ma kamata ka yi ba. Mu har ga Allah, tunda mu ka shigo fim, sana’a mu ka ɗauke ta, kuma ita mu ke yi.”

“So, don Allah don Annabi in za ku yi magana ku riƙa yi mana adalci. Mu duk da son iyayen mu mu ka shigo fim. Ni sai da iyaye na su ka yarda in yi fim sannan na shigo saboda sun san cewa sana’a zan je yi, kuma shi na ke yi. Ban masu abin magana ko abin faɗi ba.

“In ku na magana ku riƙa yi mana adakci. Mu mata mun shigo harkar fim da yawa, sana’a mu ke yi. So, da dama in za mu yi wa kan mu adalci, ɓata-garin mu ba ‘yan fim ba ne, ‘mu na fim’ ne; akwai ‘yan fim, akwai ‘mu na yin fim’.

“In an tashi kullum a ce matan fim, matan fim; su matan fim ba su da mafaɗa ne? Kullum mu a haka mu ke?”

Jarumar ta ce, “Na yi magana, wasu su na cewa ai ba duka aka ce ba, wasu daga cikin mata. Don Allah duk ‘headline’ ɗin da ake ‘posting’ ɗin wannan maganar a TikTok a je a duba. An ce duka matan ‘yan fim sun fi ƙarfin iyayen su, cewar kaza. Me ya sa da aka tashi rubutun ‘headline’ ɗin maganar ba a ce wasu daga cikin matan ‘yan fim sun fi ƙarfin iyayen su ba?

“Me ya sa da aka tashi rubutun ba a ce wasu daga cikin matan ‘yan fim su ma shigowa sana’a ba da son iyayen su ba, me ya sa?

“No, ya kamata dukkan mu mun waye. Ya kamata mu san cewa lokaci ya wuce da za a ce mutum ɗaya ya yi magana an ce wasu daga cikin matan ‘yan fim, ko wani guda ɗaya ya ce abu a ce ɗaya daga cikin ‘yan fim.

“Tun baya kafin mu shiga harkar fim, ɗan fim bai taɓa yin wani abu an ware mutum ɗaya an ce shi ya yi ba, za a ce ‘yan fim duka, in an tashi ba za a zagi ɗaya ba, za a ce ‘yan fim ne duka.

“So, maganar a ce wasu ma bai taso ba. Mu da mu ke cikin sana’ar mun sani cewa wani bai taɓa yin laifi an zagi ɗayan mu ba, dukkan mu ake haɗawa a zaga. In mun san dukkan mu ake haɗawa a zaga, har a cikin mu me wani zai yi magana ya ce wasu, kuma a ce maganar shi ta tafi ‘purposely based on’ waɗanda ya yi magana? Generalising ake yi mana.

“Duk abin da ya faru a Kannywood a kan mutum ɗaya, za a yi generalising a zage mu ne mu duka, mun sani. Mu ba mu ba mu ce kowa ya kare mu ba, mu ba mu ce mazan da ke ciki in sun tashi intabiyu su kare mu ba, kuma bai kamata su riƙa faɗin kalmar da sai bayan sun yi intabiyu a zage mu da shi ba.

“Yes, alhamdu lillahi iyayen mu ba ‘yan soshiyal midiya ba ne, ba su yi. Amma abokan arziki da ‘yan’uwan mu duk su na gani, kuma su na nuna mana, ba mu jin daɗi. Saboda ba a ware mu, ba a ware wancan, ba a ware wancan, duka ake haɗa mu.

“So, don Allah ‘point of correction’ masu magana, ku daina ce min an ce min an ce wasu. Ku je ku duba ‘headline’ ɗin da aka yi rubutu ba a ware kowa ba, an ce duka matan da ke fim an ce kaza a kan ta. Akwai wanda aka ware an ce wasu daga cikin matan fim ga abin da su ke yi?”

“So, wani abu da kullum mutanen gari su ke kallon mu da shi, matan ‘yan fim ‘yan iska ne, matan ‘yan fim ‘yan banza ne, matan ‘yan fim kaza, matan ‘yan fim kaza. Wannan tunanin su ne, ba su san mu ba. Idan ku mazan ‘yan fim Allah ya haɗa mu da ku gaba ɗaya, mu ka zama ‘yan’uwan juna, sana’a ɗaya, ba ku nemi kun kare mana mutunci ba, ku ne in kun yi hira za ku faɗi wata kalma da za a zage mu, to ina za a yabe mu?

“A cikin mu an zage mu, sai wani ya zage mu a waje, za mu ji haushi? Idan mazan da ba ‘yan fim ba su na zagin mu, ba su san mu ba mu na yi masu uziri, amma mu da ku ke cikin mu kun fito kun zage mu, ku ɗauka mu idan ƙannen ku ne uwar mu ɗaya, uban mu ɗaya, wasu kalmomin da ku ke jefa mana a ci gaba da zagin mu a gari, shi za ku riƙa jefa mana? Ba mu ce ku kare mu ba, amma sai ku bar mu da abin da iya ‘yan gari su ke faɗa a kan mu.

“An ce wani sakamakon sai a lahira. So, sai ku bar mu iya kallon da su ke yi mana da iya tunanin su a kan mu. Allah kaɗai ya san me mu ke yi.

“Wani ma har ya na maganar fim sana’a ce, amma mata da yawa da su ke cikin ‘yan fim ba su da kunya ba su da kaza, su na bayyana tsiraicin su. Kai da ka ke magana mata nawa ka ke kallo a soshiyal midiya wanda ba ‘yan fim ba su ke abin da ‘yar fim ko kuɗi ka ba ta ba za ta yi ba? Ba faɗa ba ne kawai, ba mun riga mun yi suna ba ne a duniya? Mun riga mun yi suna a wurin mutane, mutane su na kallon mu mutanen banza. Mutane dubu nawa su ke abin da ko kuɗi aka ba mu ba za mu yi ba? Ba su da adadi a duniya. Wallahi ko kuɗi aka ba mu abin da wasu matan waɗanda ba ‘yan fim ba su ke yi, ba za mu yi ba, wa ke zagin su?

“Yes, ka sani, idan Allah ya kai ka wani matsayin sai an zage ka, idan ma ba a zage ka ba, ba ka kai ba, mun san da wannan.

“Amma kullum abin da na ke magana a nan shi ne, duk wanda ke sana’ar fim, idan bai kare ‘yar fim ba, bai kamata ya bar kalmar da za a zagi ‘yar fim da ita ba. Saboda ba mu jin daɗi, abokan arzikin mu, ‘yan’uwan, ba zan saka iyayen mu ba, kamar yadda na ce ba ‘yan soshiyal midiya ba ne, babu abin da su ka sani a kan midiya.

“So, na ga wasu sun saka baki, wai a ce wasu. Ku je ku duba ‘headline’ ɗin kafin ku ce wasu. Idan da na ga masu rubutun da masu ‘posting’ ɗin a lokacin sun ware sun ce wasu daga cikin matan ‘yan fim su na kaza ko sun fi ƙarfin iyayen su a kan kaza, wallahi ko magana ba zan yi ba, ƙala ba zan ce ba. Saboda wani abu wanda ya na faruwa, ya daɗe ya na ɓata min rai waɗannan abubuwan su ke faruwa. Saboda za ka ga babu dalili ai, ko wani magana a kan macen fim, macen fim, macen fim, macen fim? Yes, ‘yan waje su na yi, mu na yi masu uzuri, wala’allah tunanin su ne a kan mu haka. Amma don Allah don Annabi mazan da ku ke cikin mu ku riƙa yi mana adalci. Don Allah idan ba za ku faɗi alkhairi a kan mu ba, ku riƙa yi mana shiru.

“Wallahi za mu yi aure. Yanzu ka zo ka ce mace ‘yar fim ba ta da tarbiyya, ba a ware wasu ba an haɗa mu gaba ɗaya, yaushe ka ke tunanin wane namijin ƙwarai ne zai auri mace da ba ta da tarbiyya? Wane namijin ƙwarai ne zai auri wadda ta fi ƙarfin iyayen ta? Wane namijin ƙwarai ne zai auri wadda ba ta jin maganar iyayen ta? Wane namijin ƙwarai ne zai auri wadda bai isa ba, ba ki da tarbiyya, ba ki jin maganar iyayen ki, ba wanda ya isa gaya miki ki ji? Wane namijin ƙwarai ne zai aure ki?

Hannatu Bashir fitacciyar jaruma ce kuma furodusa a Kannywood 

“To a bar shi ma kin samu namijin ya aure ki, sai kuma nan gaba a riƙa ɗauko irin waɗannan kalmomin ana dawowa, lokacin ‘ya’yan mu sun taso, sai su ga cewa mu da ga yadda mu ke? Ko ga abin da mu ke yi wa iyayen mu, which ba gaskiya ba ne. Kuma a ce ran mu ba zai ɓaci ba? Ya kamata ran mu ya ɓaci. Ya kamata kuma mu riƙa yi wa kan mu magana mu na yi wa kan mu adalci.

“Don Allah maza idan za ku faɗi abu a kan mu, don Allah, don Annabi in ba za ku faɗi alkhairi kan mu ba, ku taimaka ku yi mana shiru. Babu wata mace da ta taɓa intabiyu da ta bar wa wani namiji abin zagi. Amma ‘majority’ hirar maza ko a ce ba a san inda ‘yar fim ta ke samun kuɗi ba… Me ya yi zafi ne? Allah ya sa mu dace.”

Loading

Tags: Adam A. ZangoHannatu Bashirmartani
Previous Post

Gwamnatin Tinubu ga gwamnonin PDP: Matsalar Nijeriya ba ta kai ta Venezuela ba

Next Post

Shugaban MOPPAN, Habibu Barde, zai aurar da ɗan sa ranar Asabar

Related Posts

An naɗa Shehu Hassan Kano shugaban riƙo na MOPPAN
Labarai

An naɗa Shehu Hassan Kano shugaban riƙo na MOPPAN

June 3, 2025
MOPPAN ta ba gwamnan Kebbi lambar yabo a madadin ‘yan fim
Labarai

MOPPAN ta ba gwamnan Kebbi lambar yabo a madadin ‘yan fim

June 2, 2025
Ƙungiya ta ja kunnen gwamnatin Kano kan dakatar da finafinan Kannywood 22
Labarai

Ƙungiya ta ja kunnen gwamnatin Kano kan dakatar da finafinan Kannywood 22

May 20, 2025
Hukuma ta rufe gidajen gala a Kano har sai bayan Ramadan
Labarai

Gwamnatin Kano ta dakatar da haska finafinan Kannywood 22 a intanet da talbijin 

May 19, 2025
Labarai

Gwamnan Kano ya ɗauki nauyin ‘yan Kannywood 5 zuwa Hajjin bana

April 17, 2025
Sabuwa, matar Ɗanmaraya Jos, ta rasu
Labarai

Sabuwa, matar Ɗanmaraya Jos, ta rasu

March 28, 2025
Next Post
Shugaban MOPPAN, Habibu Barde, zai aurar da ɗan sa ranar Asabar

Shugaban MOPPAN, Habibu Barde, zai aurar da ɗan sa ranar Asabar

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!