ALLAH ya azurta matashin mai ɗaukar hoton bidiyo a Kannywood, Ibrahim Wassh da ‘ya mace.
Maiɗakin sa, Sakina, ta haihu da misalin ƙarfe 3:00 na rana a ranar Lahadi da ta gabata a babban asibitin gwamnati da ke Kawo, Kaduna.
An raɗa wa jaririyar suna Fatima, amma a riƙa kiran ta da Zahra.
A yau Lahadi za a yi taron suna a gidan Ibrahim da ke Layin Mai Unguwa a Unguwar Dosa, Kaduna.

Zahra ita ce ‘yar sa ta biyu, domin akwai yayar ta, wato Meera.
Allah ya raya su, ya kuma albarkaci rayuwar su.