• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Wednesday, July 23, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Gwamnatin Tarayya za ta fara tace finafinan da ake yaɗawa ta intanet

by DAGA IRO MAMMAN
November 11, 2021
in Labarai
0
Alhaji Adedayo Thomas

Alhaji Adedayo Thomas

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

GWAMNATIN Tarayya ta bayyana cewa nan ba da jimawa ba za ta fara sa hannu kan irin finafinan da ake shiryawa ana yaɗa su ta hanyar intanet ba tare da an tace su ba.

Irin waɗannan finafinan, har ma da waƙoƙi, ana kiran su da Turanci ‘Over the Top content’ (OTT a taƙaice). 

Babban Daraktan Hukumar Tace Finafinai ta Ƙasa (National Film and Video Censors Board, NFVCB), Alhaji Adedayo Thomas, shi ne ya bayyana haka ga manema labarai a otal ɗin KAP Hub da ke Ikeja a Legas.

Ya ƙara da cewa hukumar ta na aiki ba ji ba gani wajen ganin ta riƙa sa ido kan ƙaruwar ayyukan da ake shiryawa ana yaɗa su ba tare da an tace su an saka su a rukunnan kallo da su ka dace ba.

Ya ce hukumar za ta fito da tsarin hukunta masu karya dokar hakan.

A cewar sa, “Cigaban da ake samu wajen inganci da yanayin finafinan da ake shiryawa tare da isar da su ga jama’a ya inganta cuɗanyar da jama’a ke yi sannan ya ƙarfafa yaƙi da ake yi da masu satar basira tare da haɓaka hanyoyin samun kuɗaɗen shiga da kuma faɗaɗa kasuwanci na abaubuwan da ake ƙirƙira.

“Wannan shi ya sanya Hukumar Finafinai ta ɗauki batun saka hannu kan ababen OTT da matuƙar muhimmanci.”

Haka kuma babban daraktan ya bayyana cewa hukumar ta tace finafinai ta na nan ta na shirin gudanar da wani babban taro inda za a tattauna kan irin waɗannan finafinan da ake ɗorawa a intanet. 

Yayin da ya ke bayyana manufar taron, wanda ya ce na kwana biyu ne, Thomas ya ce za a shirya taron ne don a samar da kyakkyawan yanayi ga masu shirya irin waɗannan finafinan. 

Ya ce, “Za a yi taro na kwana biyu kan hajar ƙirƙira ta zamani da ake shiryawa a Nijeriya don a tattauna al’amuran da za su bada dama a inganta harkar kasuwanci a masana’antar.”

Shugaban NFVCB, Alhaji Adedayo Thomas, ya na yi wa ‘yan jarida taron da za a yi, a otal ɗin KAP Hub da ke Ikeja, Legas, a yau

Mujallar Fim ta fahimci cewa za a gayyato kamfanonin yaɗa finafinai a kafofin sadarwa na zamani zuwa taron, ciki har da Netflix, Amazon Prime, Showmax, Telcos da ma wasu.

Ana sa ran cewa a taron za a yi maganganu kan duk wani abu da ake gani ko ake tunani a kan sa dangane da yadda za a haɓaka harkar shirya finafinai a Nijeriya.

Loading

Tags: adedayo thomascensorshipKannywoodNational Film and Videos Censors BoardNetflixNFVCBOTTOver the Top content
Previous Post

Yakubu Lere ya maka shugaban Vision FM Umar Farouk Musa a kotu ya na neman diyyar N20m

Next Post

Nijeriya ta jaddada sadaukarwa ga yarjejeniyar magance bala’o’i ta Sendai a taron COP26

Related Posts

Allah ya yi wa mahaifiyar darakta Salisu Mu’azu rasuwa
Labarai

Allah ya yi wa mahaifiyar darakta Salisu Mu’azu rasuwa

July 17, 2025
Hukumar Shari’a da Hukumar Tace Finafinai za su haɗa gwiwa don tsaftace tarbiyya a Kano
Labarai

Hukumar Shari’a da Hukumar Tace Finafinai za su haɗa gwiwa don tsaftace tarbiyya a Kano

July 11, 2025
Jarumin Kannywood, Baba Ƙarami ya yi magana kan ganin sa da aka yi kan keken guragu 
Labarai

Jarumin Kannywood, Baba Ƙarami ya yi magana kan ganin sa da aka yi kan keken guragu 

July 10, 2025
Tsohuwar jarumar Kannywood, Halisa tana neman addu’a
Labarai

Tsohuwar jarumar Kannywood, Halisa tana neman addu’a

July 9, 2025
Mawaƙin Manzon Allah, Abdullahi Ɗan Gano ya rasu
Labarai

Mawaƙin Manzon Allah, Abdullahi Ɗan Gano ya rasu

July 7, 2025
MOPPAN ta yi wa al’ummar Kano ta’aziyyar Aminu Ɗantata 
Labarai

MOPPAN ta yi wa al’ummar Kano ta’aziyyar Aminu Ɗantata 

June 29, 2025
Next Post
Hajiya Sadiya Umar Farouq

Nijeriya ta jaddada sadaukarwa ga yarjejeniyar magance bala'o'i ta Sendai a taron COP26

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!