• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Thursday, May 14, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Hukumar Naƙasassu: Na cika alƙawari, inji Minista Sadiya

by DAGA WAKILIN MU
August 26, 2020
in Nijeriya
0
Hajiya Sadiya Umar Farouq tare da Shugaba Muhammadu Buhari

Hajiya Sadiya Umar Farouq tare da Shugaba Muhammadu Buhari

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram
Ministar Harkokin Agaji Da Jinƙai, Hajiya Sadiya Umar Farouq, ta bayyana cewa a yanzu sabuwar Hukumar Naƙasassu ta Ƙasa, wato ‘National Disability Commission’, ta riga ta kafu bayan amincewa da naɗa shugabannin ta da Shugaba Muhammadu Buhari ya yi a ranar Litinin, 24 ga Agusta, 2020.
 
A cikin wata sanarwa da hadimar ta a ɓangaren aikin jarida, Hajiya Halima Oyelade, ta bayar a ranar Alhamis, ministar ta ce tun daga naɗin ta a bara ta sha alwashin tabbatar da ganin an kafa wannan Hukumar Naƙasassu ta Ƙasa kuma ta fara aiki. 
 
Ta ce, ‘’Wannan ranar farin ciki ce a gare ni wadda buri na ya cika, ganin cewa wani sashe na mutane masu matuƙar buƙatar tallafi waɗanda na ke jin tausayin su, a ƙarshe sun samu hukuma tasu ta kan su, har an naɗa mata shugabanni waɗanda za su tafiyar da al’amurran ta, kuma ta kare haƙƙoƙin su, sannan ta sama masu kyakkyawan yanayi da za su inganta rayuwar su har su bada tasu gudunmawar ga cigaban al’umma baki ɗaya.”
 
Ministar ta miƙa godiyar ta ga Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari saboda rattaba hannu da ya yi kan Dokar Hana Nuna Wariya Ga Naƙasassu ta Shekarar 2019 a bara, wadda ta bada damar a kafa hukumar.
 
Sadiya Umar Farouq ta ce: ‘’Ta hanyar amincewa da naɗin shugaba da Babban Sakatare da sauran membobin cibiyar gudanarwar hukumar, Mai Girma Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya ƙara nuna sadaukarwar sa ga batun inganta rayuwar mutane marasa galihu a Nijeriya, kuma ya ba su damar su ma su ci moriyar dukkan haƙƙoƙin su a matsayin su na ‘yan Nijeriya.”
 
Ta taya murna ga naƙasassun da ke Nijeriya waɗanda ta ce yawan su ya kai mutum miliyan 30 saboda wannan babbar nasara da aka samu, kuma ta yi kira a gare su da su yi amfani da wannan dama da aka sama masu.
 
Hajiya Sadiya ta ce: ‘’Ina taya murna ga ‘yan’uwa na maza da mata waɗanda ke rayuwa da wata naƙasa a Nijeriya saboda wannan cikar buri, kuma ina kira a gare ku da ku yi amfani da damar samun wannan hukuma wajen haɗa kan ku don gina rayuwa mai albarka.”
 
Har ila yau, ministar ta taya murna ga shugabannin hukumar da aka naɗa tare da yin kira a gare su da su yi aiki tuƙuru.
 
Ta ce, “Ina taya ku murna sosai, kuma ina kira a gare ku da ku ɗauki wannan wannan naɗi naku a matsayin wata dama da ku ka samu ta zama shugabanni na farko na hukumar, don haka ku shimfiɗa fandeshi mai ƙarko na hukumar, tare da tunanin cewa samun ingancin rayuwar mutum sama da miliyan 30 da ke fama da naƙasa a Nijeriya yanzu ya danganta kan yadda ku ka aiwatar da aikin ku.”
 
Da zaran Majalisar Dattawa ta amince da naɗin, hukumar za ta shiga aiki gadan-gadan, inji ta.
 
Minista Sadiya ta ce, ‘’Ayyukan hukumar sun haɗa da fito da tsare-tsare da manufofin da su ka dace tare da aiwatar da su don ilmantar da naƙasassu da kyautata rayuwar su; tsara hanyoyin inganta rayuwar naƙasassu, da kuma kyautata rayuwar su ta hanyar sauya tunanin mutane su daina yi wa naƙasassu kallon banza.”

Loading

Previous Post

‘Gidan Kashe Ahu’ da Ranar Harshen Hausa ta Duniya

Next Post

Zaɓen Edo: INEC za ta yi amfani da rajistar 2019, inji kwamishina

Related Posts

Yadda CBN ke tallabe da tattalin arzikin Nijeriya, yayin sa farashin ɗanyen mai ke faɗuwar-‘yan-bori a kasuwa
Nijeriya

Yadda CBN ke tallabe da tattalin arzikin Nijeriya, yayin sa farashin ɗanyen mai ke faɗuwar-‘yan-bori a kasuwa

November 7, 2025
Shirin ƙarfafa jari: CBN ya shawarci bankuna marasa ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji
Nijeriya

Shirin ƙarfafa jari: CBN ya shawarci bankuna marasa ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji

November 2, 2025
Bankin CBN ya yunƙuro: Naira ta hana dala numfashi mai ƙarfi a ƙarshen Oktoba
Nijeriya

Bankin CBN ya yunƙuro: Naira ta hana dala numfashi mai ƙarfi a ƙarshen Oktoba

November 2, 2025
Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje
Nijeriya

Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje

October 29, 2025
Tinubu ya yi adalci ga dukkan yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai
Nijeriya

Tinubu ya yi adalci ga dukkan yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai

August 31, 2025
Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar da Sababbin Cibiyoyin Maganin Ciwon Daji

July 24, 2025
Next Post
Zaɓen Edo: INEC za ta yi amfani da rajistar 2019, inji kwamishina

Zaɓen Edo: INEC za ta yi amfani da rajistar 2019, inji kwamishina

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!