• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Wednesday, May 6, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Jagorar Matan APC ta Kaduna, Maryam Suleiman, ta ragargaji El-Rufai, ta ce komawar sa SDP kuskure ne

* Na riga El-Rufa'i sanin Gwamna Uba Sani, inji ta

by IRO MAMMAN
March 26, 2025
in Nijeriya
0
Jagorar Matan APC ta Kaduna, Maryam Suleiman, ta ragargaji El-Rufai, ta ce komawar sa SDP kuskure ne

Hajiya Maryam Suleiman, Jagorar Matan APC

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

JAGORAR Matan jam’iyyar APC ta Jihar Kaduna, Hajiya Maryam Suleiman, ta bayyana cewa ta dawo daga rakiyar tsohon gwamna Malam Nasir El-Rufai, ta ce barin jam’iyyar da ya yi babban kuskure ne.

Maryam, wadda ta hannun damar El-Rufa’i ce a da, an dakatar da ita daga APC kwanan baya saboda sukar Gwamna Uba Sani da ta yi. Ta ce yanzu ta yi nadama, kuma tana ba shi haƙuri.

A cewar ta, abin da ta aikata yarinta ce, amma Uba Sani mutum ne mai jinƙai kuma ya yafe mata.

Ta ce ba ta fahimci abubuwan da suka jawo ta soki Uba ba, “amma bayan na gane kuskure na, sai na ba shi haƙuri,” inji ta.

Ta ce: ‘’Na faɗa masa cewa abin da na yi yarinta ce kuma a gaskiya ban fahimci abubuwan ba ne. Kowa ya san cewa ni mai sadaukarwa ce ga jam’iyya. Na gane kurakurai na kuma na gyara.”

Laƙabin Hajiya Maryam a da shi ne ‘Maryam Mai Rusau’ saboda alaƙar ta da El-Rufa’i, to amma yanzu tana kiran kan ta ne da ‘Maryam Mai Ginau’ domin nuna sabuwar alaƙar ta da gwamnatin Uba Sani.

Jagorar Matan ta ce gwamnatin El-Rufa’i ta tafka kurakurai da yawa, musamman wajen rushe kasuwanni da kuma korar malaman makarantun firamare.

Ta ce: “A gaskiya, mutane sun yi kukan waɗannan shirye-shiryen kuma an cuci jama’ar da abin ya shafa. Wasu ma sun rasa ran su. Hanyar cin abincin wasu ta toshe.

‘’Idan an kwatanta da Gwamna Uba Sani kuwa, za a ga shi mai tausayi ne. Mutum ne mai son ya taimaki mutane ko da bai san su ba. Akwai ɗimbin bambanci tsakanin sa da tsohon gwamna.”

Hajiya Maryam ta ƙara da cewa ta san Uba Sani tsawon lokaci tun kafin ya zama Sanata. Ta ce: ‘’Na riga Malam Nasir El-Rufa’i sanin shi. Mutum ne mai kirki wanda a ko yaushe yana neman yadda zai kyautata rayuwar talakawa.’’

Jagorar Matan ta ce babu wani tasiri da SDP za ta yi domin yanzu take koyon ta-ta-ta a fagen siyasa kuma ba a gama sanin ta ba.

“Ba zan taɓa komawa waccan jam’iyyar ba saboda ni cikakkiyar ‘yar APC ce,” inji ta.

Loading

Tags: APCGwamna Uba SaniKadunaMaryam Suleiman
Previous Post

Gwamnati ta ba da Litinin da Talata a matsayin ranakun hutun Ƙaramar Sallah

Next Post

Sabuwa, matar Ɗanmaraya Jos, ta rasu

Related Posts

Yadda CBN ke tallabe da tattalin arzikin Nijeriya, yayin sa farashin ɗanyen mai ke faɗuwar-‘yan-bori a kasuwa
Nijeriya

Yadda CBN ke tallabe da tattalin arzikin Nijeriya, yayin sa farashin ɗanyen mai ke faɗuwar-‘yan-bori a kasuwa

November 7, 2025
Shirin ƙarfafa jari: CBN ya shawarci bankuna marasa ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji
Nijeriya

Shirin ƙarfafa jari: CBN ya shawarci bankuna marasa ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji

November 2, 2025
Bankin CBN ya yunƙuro: Naira ta hana dala numfashi mai ƙarfi a ƙarshen Oktoba
Nijeriya

Bankin CBN ya yunƙuro: Naira ta hana dala numfashi mai ƙarfi a ƙarshen Oktoba

November 2, 2025
Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje
Nijeriya

Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje

October 29, 2025
Tinubu ya yi adalci ga dukkan yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai
Nijeriya

Tinubu ya yi adalci ga dukkan yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai

August 31, 2025
Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar da Sababbin Cibiyoyin Maganin Ciwon Daji

July 24, 2025
Next Post
Sabuwa, matar Ɗanmaraya Jos, ta rasu

Sabuwa, matar Ɗanmaraya Jos, ta rasu

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!