A RANAR Asabar mai zuwa, 11 ga Nuwamba 2023 za a ɗaura auren jarumar Kannywood ɗin nan Rashida Adamu Abdullahi Maisa’a tare da masoyin ta, Aliyu Adamu (Sardaunan Matasan Goza).
Katin gayyatar ɗaurin auren da mujallar Fim ta gani ya nuna cewa za a ɗaura auren a gidan mahaifin ta da ke layin Malam Bello a unguwar Daurawa, daura da Titin Maiduguri, a cikin garin Kano, da misalin ƙarfe 9 na safe.
Sanarwar ɗaurin auren ta zo wa ‘yan fim da bazata, domin kuwa ba kowa ba ne ya san da maganar.
Tuni dai jama’a daga ciki da wajen masana’antar shirya finafinan su ka shiga yi wa amarya Rashida fatan alheri tare da taya ta murna a game da wannan abin farin cikin.