An buɗe taron bikin bajekolin finafinai na Afirika karo na 8 wanda aka saba gudanarwa a duk shekara, wato ‘Kano Indigenous Languages of Africa Film Market & Festival.’
An fara gudanar da bikin ne a jiya Litinin 25 ga Nuwamba 2024 inda za a shafe tsawon kwanaki 5 ana yi.
A rana ta farko dai an buɗe taron ne a ɗakin lakcoci a sashin koyar da aikin jarida na Jami’ar Bayero in da manyan masana akan aikin jarida da kuma harkar fim suka gabatar da jawabai na tsawon wuni guda.
Haka nan a wani ɓangare kuma an buɗe taron hosarwa akan harkar fim da kasuwancin sa wanda yake shi ɓangare biyu ne, akwai babban aji da kuma ƙaramin aji a sashin koyar da ilimin harkar kasuwanci na Dagote duk dai a cikin Jami’ar Bayero.
Da yamma kuma an gudanar da taron liyafar maraba da baki a gidan cin abinci na Gusto dake cikin Unguwar Nassarawa G R A.
A wajen liyafar cin abincin dai shugaban gudanar da taron.l, Malam Abdulkareem Muhammad, ya gabatar da jawabin maraba da baƙi inda a cikin jawabin yake cewa:
“Muna godiya ga Allah da ya nuna mana wannan rana da za a fara wannan taro na Kalankuwar Afirika wanda har ma ya zama al’adar mu a duk shekara Allah yana bamu damar gudanar da shi. Kuma abin farin ciki da alfahari baya ga ilimin da ake samu taron ya zama wani dandamali na sada zumunta a tsakanin mu, da kuma ƙulla abota.
“A yanzu ga shi mun haɗu a waje guda cikin jin daɗi da farin ciki tare da rungumar juna. Kuma ko ba komai wannan abin alfahari ne a gare mu mu ‘yan Afirika da muke yare da al’adu mabambanta yau ga shi mun haɗu domin musayar ra’ayi da kuma sada zumunta. Muna yi wa baƙin mu maraba da suka zo daga ƙasashe masu nisa da waɗanda suka zo daga kusa kamar maƙwaftan mu Nijar da Kwatano.
“Haka nan muna yin maraba da baƙin mu da suka zo daga jihohi daban-daban har ma waɗanda suke nan garin Kano. Mun gode Allah da ya sa a yi taro lafiya a gama lafiya, kuma Allah ya mayar da kowa gidan sa lafiya.”
Taron dai ya samu halartar Kwamishinan Yaɗa Labarai na Jihar Kano, Baba Halilu Dantiye, da Kwamishiyar Ma’aikatar Al’adu da Yawon Buɗe Ido, Hajiya Ladidi Ibrahim Garko, tare da sauran manyan baƙi.