HUKUMAR Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta ja hankalin jama’a cewa ba ta san da zaman wata manhaja da wasu ‘yan damfara su ka buɗe da sunan ɗaukar ma’aikatan zaɓe na wucin-gadi ba.
Sakataren Yaɗa Labarai na hukumar, Mista Rotimi Oyekanmi, shi ne ya yi wannan gargaɗin a ranar Talata a Abuja.
Ya ce tuni INEC ta rufe shafin manhajar ta ta ɗaukar ma’aikatan zaɓe, kamar yadda ta yi bayani a baya.
A cikin Satumba ne dai INEC ta yi sanarwar cewa za ta buɗe manhajar a ranar 14 ga Satumba, 2022, kuma ta rufe ta a ranar 14 ga Disamba, 2022.
Oyekanmi ya ce: “Wannan shafin manhaja na intanet na bogi ne, ba na INEC ba ne. Saboda an rufe shafin manhajar INEC na ɗaukar ma’aikatan wucin-gadi tun a ranar 14 ga Disamba, 2022.”
Ya bayyana sunan manhajar ta bogi da: URL-http://www.yournewclaims.com/INEC/recruitment, cewa ta bogi ce kawai kuma a nisance ta.
A wani labarin kuma an samu tabbacin cewa akwai katin rajistar zaɓe har milyan 6.7 da har yanzu ba a karɓa ba a cikin wasu jihohi 17.
Rashin karɓar katin da aka yi rajista dai na ɗaya daga cikin abin da ke haifar da matsalar rashin zuwa a jefa ƙuri’a, kamar yadda INEC ta tabbatar cewa a zaɓen 2019 mutum miliyan 82 ne ke da rajistar zaɓe, amma mutum milyan 28.6 kaɗai su ka fita su ka jefa ƙuri’a.
Duk da yawan masu jefa ƙuri’a a Jihar Legas, waɗanda su ka yi zaɓe a jihar ba su cika miliyan biyu ba.