• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Friday, July 18, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Minista ya sake jaddada ƙudirin sabunta kayan aikin watsa labarai na gwamnati

by WAKILIN MU
April 17, 2025
in Nijeriya
0
Minista ya sake jaddada ƙudirin sabunta kayan aikin watsa labarai na gwamnati

Minista Mohammed Idris yana gabatar da jawabi a taron

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

MINISTAN Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya sake jaddada aniyar Gwamnatin Tarayya ta sabuntawa da kuma inganta dukkanin kayan aikin watsa labarai na gwamnati, a wani ɓangare na ƙoƙarin ta na gyara fagen yaɗa labarai a Nijeriya.

Mai taimaka wa ministan kan harkokin yaɗa labarai, Rabi’u Ibrahim, ya faɗa a cikin takarda ga manema labarai cewa Ministan ya bayyana haka ne a ranar Alhamis, yayin da yake jawabi a Zauren Taron Manema Labarai da Ministoci na Shekarar 2025, karo na shida, wanda aka gudanar a Cibiyar ‘Yan Jarida ta Ƙasa da ke Abuja.

Ministan, wanda bai daɗe da dawowa daga Babban Taro Da Bita na Ƙungiyar Masu Watsa Labarai ta Ƙasa (NAB) da aka gudanar a birnin Las Vegas na ƙasar Amurka ba, ya ce taron – mai taken “Fasaha, Madosa, Makoma” – ya ƙunshi musayar ra’ayoyi daga ƙwararru a fannin fasaha da watsa labarai daga sassa daban-daban na duniya.

Waɗanda suka take wa Ministan sawu a tafiyar su ne jagororin hukumomin yaɗa labarai da wayar da kai da ke ƙarƙashin ma’aikatar sa.

Alhaji Mohammed Idris yana jawabi a taron

Ya yi zama daban-daban tare da ƙwararru inda suka tattauna kan yadda za a inganta ƙwarewa da kuma kayan aiki na zamani na kafafen yaɗa labarai na gwamnatin Nijeriya.

Ya ce: “Ina sanar da ku waɗannan abubuwan ne domin jaddada ƙudirin gwamnatin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu na ganin an samu cigaba mai ɗorewa a fannin watsa labarai a ƙasar nan.

“Wannan ne ma ya sanya muke gudanar da irin wannan taron bita na ministoci, da kuma shirin ƙaddamar da Taron Tattaunawa da Jama’a a sassan ƙasar nan nan gaba kaɗan.”

Idris ya kuma bayyana halartar da ya yi a Taron Kasuwanci na Nijeriya da aka yi a birnin Paris, ƙasar Faransa, wanda kamfanin Business France ya shirya.

A gefen taron, Idris ya gana da manyan jami’an hukumar UNESCO domin ƙara inganta shirin kafa Cibiyar Ilimin Kafofin Watsa Labarai a birnin Abuja.

A cewar sa, wannan cibiyar za ta taimaka gaya wajen bunƙasa hazaƙar ‘yan jarida da kuma gina sahihin tsarin yaɗa labarai mai inganci a ƙasar nan.

Ya ce: “Cibiyar za ta taka muhimmiyar rawa wurin ƙara ƙarfin gwiwa da ingancin aikin ‘yan jarida a Nijeriya.”

Idris ya ƙara da cewa shirye-shiryen da ake yi kamar wannan taron bita da kuma Taron Tattaunawa da Jama’a da ke tafe, yana daga cikin dabarun gwamnatin don ƙarfafa gaskiya, ƙarfafa tattaunawa tsakanin gwamnati da al’umma, da kuma ƙarfafa amincewa a tsakanin ɓangarorin biyu.

A yayin taron, Ministan Wutar Lantarki, Cif Adebayo Adelabu, ya yi bayani kan matakan da ake ɗauka don gyara ɓangaren wutar lantarki domin tallafa wa shirin gwamnati na bunƙasa masana’antu da tabbatar da isasshiyar wutar lantarki ga ‘yan Nijeriya.

Loading

Tags: kafafen yaɗa labaraiMohammed Idris
Previous Post

Ministan Yaɗa Labarai ya kwaɗaita wa ‘yan kasuwar Faransa alfanun zuba jari a Nijeriya

Next Post

Gwamnan Kano ya ɗauki nauyin ‘yan Kannywood 5 zuwa Hajjin bana

Related Posts

Nijeriya

Tinubu yana goyon bayan Ƙananan Hukumomi su ci gashin kan su – Minista

July 11, 2025
Nijeriya

Shirin Sabunta Fata na Tinubu yana samar da damarmakin cigaba — Minista

July 10, 2025
Sauye-sauyen Tinubu suna taimaka wa farfaɗowar tattalin arzikin Nijeriya — Minista
Nijeriya

Sauye-sauyen Tinubu suna taimaka wa farfaɗowar tattalin arzikin Nijeriya — Minista

July 10, 2025
Ministoci za su fara gabatar da rahoton ayyuka a taron manema labarai
Nijeriya

Tinubu ba zai yarda hayaniyar siyasar 2027 ta ɗauke masa hankali ba – Minista

July 8, 2025
Ƙungiyoyi sun buƙaci bayanai daga ‘yan sanda kan harin da aka kai fadar Sarkin Kano
Nijeriya

Ƙungiyoyi sun buƙaci bayanai daga ‘yan sanda kan harin da aka kai fadar Sarkin Kano

July 8, 2025
SHEKARA ƊAYA BAYAN KOMAWA KAN KARAGAR MULKI: Tasirin Yadda Mai Martaba Khalifa Muhammadu Sanusi II Ya Dawo Da Martabar Masarautar Kano
Nijeriya

SHEKARA ƊAYA BAYAN KOMAWA KAN KARAGAR MULKI: Tasirin Yadda Mai Martaba Khalifa Muhammadu Sanusi II Ya Dawo Da Martabar Masarautar Kano

July 5, 2025
Next Post

Gwamnan Kano ya ɗauki nauyin ‘yan Kannywood 5 zuwa Hajjin bana

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!