• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Thursday, May 14, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Ministan Yaɗa Labarai ya yi kira ga jihohi da kada su rushe Ma’aikatun Yaɗa Labarai

by WAKILIN MU
December 14, 2024
in Nijeriya
0
Ministan Yaɗa Labarai ya yi kira ga jihohi da kada su rushe Ma’aikatun Yaɗa Labarai

Alhaji Mohammed Idris

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

MINISTAN Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya yi kira ga gwamnatocin jihohi da ke tunanin rusawa ko rage matsayin Ma’aikatun Labaran su da su sake tunani, yana mai jaddada mahimmancin su wajen hulɗa da jama’a, wayar da kai, da kuma haɗin kan al’umma.

Idris ya yi wannan kiran ne yayin taron Majalisar Ƙasa kan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai karo na 48 a Kaduna a ranar Juma’a, mai taken “Inganta Gudanar da Yaɗa Labarai don Shugabanci Mai Haɗin Kai: Ajandar Sabunta Fata.”

Ya ce, “A wannan lokaci, ina son yin roƙo mai matuƙar mahimmanci ga wasu daga cikin gwamnatocin jihohin mu, musamman kan matsayi da ayyukan Ma’aikatun Yaɗa Labarai na Jihohi.

“Kuma roƙo na shi ne: a shugabanci, ba za a taɓa musanta muhimmancin Ma’aikatun Labarai ba a matakin tarayya da jiha. Waɗannan Ma’aikatu sun zama wata gada tsakanin manufofin gwamnati da ‘yan ƙasa da aka tsara su amfana da su, ta yadda za su samar da gaskiya, da riƙon amana, waɗanda su ne ginshiƙan kowace dimokiraɗiyya mai ci gaba.”

Idris ya jaddada cewa Ma’aikatun Yaɗa Labarai suna da matuƙar muhimmanci wajen wayar da kan jama’a, yaƙi da labaran ƙarya, da tabbatar da isar da manufofi da shirye-shiryen gwamnati yadda ya kamata.

Ya bayyana ma’aikatar a matsayin “jigon dimokiraɗiyya da cigaba,” musamman a ƙasa mai ɗimbin bambance-bambance kamar Nijeriya.

Da yake magana akan Ajandar Sabunta Fata na Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, Idris ya ce wannan kira ne na shugabanci mai kawo sauyi wanda ya dogara kan haɗin kai da gaskiya.

Ya ce shugabanci ya ta’allaƙa ne ga iyawarsa na haɗawa, sadarwa, da ƙarfafa haɗin gwiwar jama’a.

Ministan ya shawarci Manajojin Watsa Labarai da su yi amfani da fasaha, ciki har da na’ura mai ƙwaƙwalwa (AI), don inganta sauri da sahihancin saƙonnin su.

Ya kuma jaddada muhimmancin muhawarar jama’a wajen gyaran manufofi, yana bada misali da tattaunawar da ake yi kan sauye-sauyen haraji da Shugaba Tinubu ya gabatar.

“A kowace dimokuraɗiyya, karfin shugabanci yana da tushe sosai a cikin ikonsa na nuna muradun jama’a. Manufofin jama’a, yayin da aka ƙera su da kyakkyawar niyya, dole ne su ci gaba da bunƙasa don biyan buƙatu da tsammanin ‘yan ƙasa,” inji Idris.

Idris ya kuma jaddada buƙatar horas da jami’an yaɗa labarai kan dabarun tabbatar da gaskiya da haɓaka haɗin gwiwa da kafofin watsa labarai don yaƙi da labaran ƙarya.

Ya bayyana cewa Shugaba Tinubu kwanan nan ya amince da sakin kuɗi don fara aiki da Cibiyar UNESCO ta Category-2 Media and Information Literacy (MIL), wacce za a kafa a Buɗaɗɗiyar Jami’ar Nijeriya (NOUN) da ke Abuja.

Ya ce, “A lokacin da labaran ƙarya, furofaganda, da rahotannin son zuciya ke iya tasiri sosai kan ra’ayin jama’a da yanke shawara, fahimtar kafofin watsa labarai yana ƙarfafa tunani mai zurfi.

“Yana taimaka wa mutane su nazarci manufar saƙonnin kafofin watsa labarai, su fahimci yanayin da aka gabatar da su, da kuma tantance sahihancin su.

“Don haka ina kira ga Kwamishinonin Yaɗa Labarai da su yi amfani da wannan cibiya mai matuƙar muhimmanci da zarar ta fara aiki domin ƙara inganta ƙwarewar ma’aikatansu wajen yaƙar labaran ƙarya,” inji shi.

Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, shi ne ya buɗe taron.

Taron ya samu halartar manyan masu ruwa da tsaki da suka haɗa da Sanata Kenneth Eze, Shugaban Kwamitin Majalisar Dattawa kan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, da Hon. Olusola Steve Fatoba, Shugaban Kwamitin Majalisar Wakilai kan Yaɗa Labarai, Wayar da Kai, Ɗa’a, da Ɗabi’u.

Loading

Tags: Ma'aikatar Yaɗa LabaraiMohammed IdrisUba Sani
Previous Post

‘Yan fim da marubuta sun fidda ni kunya a bikin ‘ya ta, inji jaruma Asma’u Sani

Next Post

Minista ya yaba da zaɓen ƙungiyoyin IPI da NUJ, kuma ya yi kira da a yi aikin jarida yadda ya dace

Related Posts

Yadda CBN ke tallabe da tattalin arzikin Nijeriya, yayin sa farashin ɗanyen mai ke faɗuwar-‘yan-bori a kasuwa
Nijeriya

Yadda CBN ke tallabe da tattalin arzikin Nijeriya, yayin sa farashin ɗanyen mai ke faɗuwar-‘yan-bori a kasuwa

November 7, 2025
Shirin ƙarfafa jari: CBN ya shawarci bankuna marasa ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji
Nijeriya

Shirin ƙarfafa jari: CBN ya shawarci bankuna marasa ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji

November 2, 2025
Bankin CBN ya yunƙuro: Naira ta hana dala numfashi mai ƙarfi a ƙarshen Oktoba
Nijeriya

Bankin CBN ya yunƙuro: Naira ta hana dala numfashi mai ƙarfi a ƙarshen Oktoba

November 2, 2025
Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje
Nijeriya

Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje

October 29, 2025
Tinubu ya yi adalci ga dukkan yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai
Nijeriya

Tinubu ya yi adalci ga dukkan yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai

August 31, 2025
Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar da Sababbin Cibiyoyin Maganin Ciwon Daji

July 24, 2025
Next Post
Minista ya yaba da zaɓen ƙungiyoyin IPI da NUJ, kuma ya yi kira da a yi aikin jarida yadda ya dace

Minista ya yaba da zaɓen ƙungiyoyin IPI da NUJ, kuma ya yi kira da a yi aikin jarida yadda ya dace

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!