Jamila Umar ta bayyana farin cikin ta kan gasar da ta ci ta Jarumar Jarumai ta 2016 a bikin mujallar Tozali da aka yi kwanan baya:
FIM: Mujallar Fim na taya ki murnar samun kyautar Tozali Awards.
JAMILA NAGUDU: To ni ma na gode, kuma na ji dadi da Fim ta taya ni murna (dariya).
FIM: Za mu iya jin wasu kyaututtuka da ki ka taba samu a baya?
JAMILA: E, amma kyaututtukan su na da yawa, kuma na san mujallar Fim ai ta na sane da dukkan irin kyaututtukan bajintar da na taba samu. Ta karshe dai ita ce ta AMMA Awards da aka yi a nan Abuja, sai kuma wannan.
FIM: Me za ki ce dangane da wannan din da ki ka samu?
JAMILA: Ina yi wa Allah (SWT) godiya, tunda na san duk da jarumtar ka da iyawar ka, ba za ka samu irin wannan kasaitacciyar kyauta ba sai da rabo da nufin Allah.
FIM: Ko ki na da sako ga Tozali, mujallar da shirya wannan kasaitaccen bikin bayar da kyaututtuka?
JAMILA: Sai godiya, domin ni dai a gaskiya Tozali ta kara shafa min tozali a idanu. Mujalla ce wacce kusan in ce maka kowace mace ke kwadayin karantawa a kasar nan. Yadda har wannan mujalla ta tuna ko ta san da ni, ai abin alfahari ne.