MURNA ba ta misaltuwa a wajen tsohuwar fitacciyar jarumar Kannywood, Maryam Aliyu Umar Ampi, a wannan makon saboda auren ɗiyar ta, Illaf, wanda za a ɗaura gobe Asabar, 27 ga Agusta, 2022.
Tsohuwar jarumar, wadda aka fi sani da Maryam Mushaqqa, ta auri Alhaji Muhamed Auwal Galadima ne a ƙasar Kamaru yau shekara 19, kuma auren ya yi albarkar ‘ya’ya da cigaban rayuwa.
Auren nasu babban misali ne na ‘yan fim masu yin aure su zauna, kuma ya karya lagon iƙirarin da wasu ke yi cewar wai ‘yan fim mata ba su zaman aure.
A tattaunawar da su ka yi da mujallar Fim a yau, Hajiya Maryam da Alhaji Auwal sun bayyana matuƙar murna kan wannan abin farin ciki da ya same su na aurar da babbar ‘yar su.

Iyayen amaryar sun kuma yi tsokaci dangane da masu cewa ‘yan fim mata ba su zaman aure.
Mushaqqa ta ce: “Assalamu alaikum. Barkan mu da safiya, ina gaishe da kowa. Ina yi wa makaranta Fim Magazine fatan alkhairi.
“Gaskiya ba zan iya misalta farin cikin da na ke ciki ba kasancewar ban saba ba, ban taɓa zaton zan yi tsawon rai har in ga wannan rana ba. So, ina cikin annashuwa da farin ciki, ina kuma addu’ar Allah ya ba su zaman lafiya, Allah ya kaɗe masu fitina. Irin ni ma na yi suriki, ka gane irin abin! Abin na da daɗi sosai, kuma abin alfahari ne.
“Allah ya sa mutu-ka-raba. Allah ya sa su yi dogon zango na rayuwa mai albarka, amin.
“Sai kuma godiya ta musamman ga maigida na da ya nuna mana ƙauna da kulawa. Allah ya saka masa da alkhairi. Allah ya sa ya gama lafiya, amin.
“Ina kuma miƙa gaisuwa ta ga ƙawaye na na Nijeriya da nan da su ka goya min baya da addu’o’i da ƙarfin su da jikin su da bakunan su masu albarka. Ina godiya.”
A kan maganar auren ‘yan fim, mahaifiyar su Illaf ta ce: “Maganar ‘yan fim ba su zaman aure, majority waɗanda su ke karanta labarai ko kuma yanzu da abubuwa su ka yawaita, komai a bayyane ya ke, su kan su in za su yi adalci sun san ba haka ba ne, domin aure kamar rai ne da shi, idan Allah ya yi zai mutu, to duk yadda ka ke son sa sai ya mutu, sai an rabu. Don haka ina yi maku fatan alkhairi. Na gode sosai.
“Sai kuma a taya mu da addu’a, Ubangiji Allah ya kawo na ‘yan baya. Dukkan ‘yan’uwa Musulmai da su ke zaune a gidajen su Allah ya ƙara masu haƙuri da zaman lafiya, waɗanda kuma ba su da gidaje – zawarawa da ‘yan matan mu – Allah ka ba su masu riƙe su bisa gaskiya. Na gode.”
A nasa ɓangaren, shi ma Alhaji Auwal ya tofa albarkacin bakin sa a kan maganar wai ‘yan fim mata ba su son zaman aure, ya ce, “A gaskiya wannan maganar ba gaskiya ba ne. Shi aure ko a Madina ma ana iya rabuwa, kuma ko wace mace da irin halin ta.

“Yau shekarar mu goma sha tara mu na tare lafiya lau. Kuma ban da ita akwai da yawa daga cikin ‘yan fim da su ke zaune a gidan aure lafiya lau. Kowace mace ta na da irin tarbiyyar da iyayen ta su ka ba ta.”
A gobe Asabar, da misalin ƙarfe 9:00 na safe, za a ɗaura auren Illaf Muhamed Auwal Galadima da angon ta, Hassan Yuguda, a garin Douala na ƙasar Kamaru.
Allah ya ba su zaman lafiya da zuri’a ɗayyiba, amin.


