BAYAN kammala zangon shugabancin Ƙungiyar Marubuta ta Nijeriya a (ANA), reshen Jihar Kano, na tsawon shekara biyu da shugaban ta, Tijjani Muhammad Musa, ya yi, ƙungiyar ta sake zaɓen shugabanni.
An gudanar da zaben a wajen taron wata-wata da ƙungiyar ta saba gudanarwa a duk Asabar ɗin ƙarshen wata a ɗakin karatu na Murtala Muhammed da ke Titin Ahmadu Bello a Kano inda a wannan watan aka yi taron a ranar 28 ga Oktoba, 2023.
An yi taron cikin kwanciyar hankali ba tare da tayar da jijiyar wuya ko wata hayaniya ba.
Dakta Murtala M. Uba ne aka zaɓa a matsayin sabon Shugaba.
Sauran su ne:
* Kamilu Ɗahiru Gwammaja – Mataimakin Shugaba
* Ibrahim Muhammad Indabawa – Sakatare
* Aliyu Abdullahi – Mataimakin Sakatare
* Sadiya Garba Yakasai – Ma’aji
* Hassan Ibrahim Gama – Sakataren Kuɗi
* Bashir A. Bashir – Jami’in Yaɗa Labarai (Hausa)
* Abba Musa Idris – Jami’in Yaɗa Labarai (Turanci)
* Sani Scholer – Jami’in Walwala
* Ayuba Muhammad Ɗanzaki – Mai Bincike (1)
* Aisha Aliyu Jibril – Mai Bincike (2)
* Jibril Adamu Jibril Rano – Mai Bada Shawara Kan Shari’a
* Zubairu M. Balannaji, Mukhtar A. Gandu, Mazhum Idris da Tijjani Muhammad Musa – Shugabanni Marasa Gafaka
A lokacin da ya ke jawabi bayan rantsuwar kama aiki, Dakta Murtala M. Uba, wanda malami ne a fannin Labarin Ƙasa (Geography) a Jami’ar Bayero, Kano, ya yi godiya ga ‘yan ƙungiyar da su ka zaɓe shi a matsayin shugaban su.
Ya ce zai ci gaba da kawo sauyi a ƙungiyar har zuwa tafarkin da ya dace duk da cewar tun bayan kafuwar ta ake ta ƙoƙarin kai ta matakin da ya dace a duniya duba da yadda ta ke da masana a fannonin ilmi daban-daban.
Ya ce ya ƙudiri aniyar samar da cigaban da kowa zai yi alfahari da ƙungiyar.