• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Friday, July 18, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Shari’a kan zargin zamba cikin aminci ta N10.3m: Lauyoyin Rarara sun gurfana a kotu

by DAGA MUKHTAR YAKUBU
April 13, 2023
in Labarai
0
Dauda Kahutu (Rarara)

Dauda Kahutu (Rarara)

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

A YAU Alhamis, 12 ga Afrilu, 2023 ne lauyoyin mawaƙi Dauda Abdullahi Kahutu (Rarara) su ka bayyana a gaban Kotun Shari’ar Musulunci da ke Rijiyar Zaki a Kano domin gabatar da kan su a matsayin masu tsaya masa a ƙarar sa da wani ɗan kasuwa ya shigar.

Idan kun tuna, mujallar Fim ta ba ku labarin yadda ɗan kasuwar, mai suna Muhammad Ma’aji, ya maka Rarara a kotun a kan kuɗi naira miliyan goma da dubu ɗari uku (N10.3m) da ya ce ya na bin sa.

Mujallar Fim ta ƙara samun bayanin cewa ɗan kasuwar ya ce ya biyo Rarara kuɗin ne sanadiyyar wayoyi da ya ke karɓa a wajen sa ya na raba wa mutane. Ya ce daga ƙarshe ya ƙi biyan shi kuɗin, kuma ya bi duk wata hanya da zai bi amma kuɗin sun ƙi fita.

A zaman kotun da ya gabata a makon jiya, kotun ta bayyana rashin gamsuwa kan yadda Rarara ko lauyoyin sa su ka gaza amsa sammacin da aka aika masa.

A wata sanarwa da ya bayar, kakakin manyan kotunan Shari’ar Musulunci na Jihar Kano, Malam Muzammil Ado Fagge, ya bayyana yadda Rarara ya dinga wasan ɓoyo da masinjan kotu don kada a ba shi sammaci. 

Ya ce: “Wannan ƙara ce wadda Muhammad Ma’aji ya shigar da Rarara, kuma ƙara ce wadda akwai mu’amulla da shi har ta naira miliyan goma kuma ya yi ya yi ya ba shi ƙuɗin amma ya ƙi.

 “Don haka mun yi amfani da doka da oda ta 9, 2021 da ta yi magana cewa idan aka nemi mutum don a ba shi sammaci ba a gan shi ba to za a iya yin amfani da shafukan sada zumunta don sanar da shi ko kuma a liƙa masa a gidan sa.

“Shi wannan mawaƙin sai wasan ɓuya ya ke yi da jami’in mu don ya ba shi sammacin amma ya ƙi yarda su haɗu, shi ya sa mu ka nemi mai unguwar sa da kuma shaidu mu ka liƙa masa a gidan sa da ke Zoo Road, domin tabbatar da bin doka wajen isar masa da saƙon kotun.”

To amma dai a yau lauyoyin Rarara sun bayyana a ƙarƙashin jagorancin Barrister G.A. Badawi, inda su ka nemi a ba su dama su yi nazarin tuhumar da ake yi wa mawaƙin domin su yi martani.

Alƙalin kotun, Mai Shari’a Halhaltul Khuza’i Zakariya, ya ba su dama, inda ya sanya Litinin mai zuwa, 17 ga Afrilu, 2023 a matsayin ranar da za a koma kotu domin ci gaba da shari’ar.

Loading

Tags: Dauda Kahutu RararaG.A. BadawiHalhaltul Khuza'i Zakariyakotun MusulunciMuhammad Ma'ajiMuzammil Ado FaggeRijiyar Zakishari'a
Previous Post

Gudun zuwa kotu, Adam A. Zango ya ba matar sa Safiyya Chalawa takardar saki

Next Post

Hukumar ‘yan sanda ta sallami jami’an ta da ke kare Rarara

Related Posts

Hukumar Shari’a da Hukumar Tace Finafinai za su haɗa gwiwa don tsaftace tarbiyya a Kano
Labarai

Hukumar Shari’a da Hukumar Tace Finafinai za su haɗa gwiwa don tsaftace tarbiyya a Kano

July 11, 2025
Labarai

Jarumin Kannywood, Baba Ƙarami ya yi magana kan ganin sa da aka yi kan keken guragu 

July 10, 2025
Tsohuwar jarumar Kannywood, Halisa tana neman addu’a
Labarai

Tsohuwar jarumar Kannywood, Halisa tana neman addu’a

July 9, 2025
Mawaƙin Manzon Allah, Abdullahi Ɗan Gano ya rasu
Labarai

Mawaƙin Manzon Allah, Abdullahi Ɗan Gano ya rasu

July 7, 2025
MOPPAN ta yi wa al’ummar Kano ta’aziyyar Aminu Ɗantata 
Labarai

MOPPAN ta yi wa al’ummar Kano ta’aziyyar Aminu Ɗantata 

June 29, 2025
Ƙungiyoyin harkar fim, KAFIGAN da MOPPAN, sun yi wa Rahama Sadau ta’aziyyar rasuwar mahaifin ta
Labarai

Ƙungiyoyin harkar fim, KAFIGAN da MOPPAN, sun yi wa Rahama Sadau ta’aziyyar rasuwar mahaifin ta

June 23, 2025
Next Post
'Yan sanda ukun da aka kora daga aiki

Hukumar 'yan sanda ta sallami jami'an ta da ke kare Rarara

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!