TUN bayan shigowar kakar zaɓen 2023 da a yanzu aka fara ake ganin kamar tafiyar ƙungiyar mawaƙa ta 13+13 ta samu matsala. Tunanin hakan ya faru ne saboda ganin yadda jiga-jigan tafiyar kowa ya kama gaban sa a wajen tafiyar siyasa.
Da man dai ba tun yanzu ba ake ganin idan har aka zo wannan lokacin to ƙungiyar za ta samu kan ta a cikin irin wannan yanayin saboda bambancin ra’ayin siyasa da ya ke tare da ‘yan ƙungiyar tun a baya, don haka ake ganin wannan tafiyar da za ta je ko’ina ba, duk da yake ta wuce lokacin da ake tunanin wargajewar ta.
A yanzu idan aka dubi tafiyar ‘yan ƙungiyar, za a ga kamar ta mutu ne ko kuma ta yi doguwar suma, saboda babu wani abu da ake gabatarwa da sunan 13+13 kamar yadda aka riƙa yi a baya. Haka ma sauran ‘yan ƙungiyar, kowa da inda ya sa gaba a harkar siyasa. Kamar shi jagoran tafiyar, Dauda Kahutu (Rarara), ya yi wani haɗin gambiza inda a matakin ƙasa ya ke tafiyar Bola Tinubu na APC, a Kano kuma ya na cikin tafiyar Sha’aban Ibrahim Sharaɗa na ADP.
Mawaƙi Aminu Ladan Abubakar Ala da jarumi Daddy Hikima sun fito takarar Majalisar Tarayya a ADP, amma a mataki na ƙasa ba mu ji su na tafiyar wani ɗan takara ba.
Umar M. Shareef tuni ya haɗe da Abdul Amart a tafiyar YBN su na ta tallar Tinubu, ƙungiyar da ba sa zama inuwa guda da 13+13 a baya, yayin da shi kuma Ali Isa Jita ya kama tallar Atiku Abubakar a mataki na ƙasa, a Jihar Kano kuma ya na cikin tafiyar NNPP ta Dakta Rabi’u Musa Kwankwaso.
Ganin halin da tafiyar 13+13 ta ke ciki a yanzu, mujallar Fim ta tambayi ɗaya daga cikin shugabannin ta, Aminu Ala, idan ƙungiyar ta samu matsala ne a yanzu.
Sai Ala ya ce: “To gaskiya ba wata matsala mu ka samu ba. Kamar yadda kowa ya sani, ita wannan ƙungiyar ta mawaƙa ce, kowa ya na da nasa ra’ayi na siyasa. To sai mu ka ce mu ajiye ra’ayi, a zo a haɗa kai don a taimaki juna a kuma taimaki jama’a. Kuma haka aka yi.
“Kowa ya ga abubuwan da mu ka yi. Ba a taɓa samun wata ƙungiya da ta taimaka wa ‘ya’yan ta da kuma jama’a ba kamar 13+13.
“To a yanzu an zo wata gaɓa ne ta siyasa, kuma kowa da nasa gwanin. Don haka sai ƙungiya ta bai wa kowa dama ya je ya yi ra’ayin sa na siyasa, idan an gama, to kowa sai ya dawo a ci gaba da tafiyar ƙungiyar. Amma dai ba matsala aka samu ba, da amincewa aka yi wannan; kowa ya je ya yi ra’ayin sa.
“Don akwai wasu ma da za ka ga ba su da wani zaɓi a siyasa. Kamar ni, duk da ina takarar Majalisar Tarayya, amma da watan Mauludi ya kama sai kuma na koma waƙoƙin da na ke yi na Mauludi ne da ake gayyata ta gari-gari. To ka ga kowa da inda ya sa gaba.
“Don haka 13+13 ta na nan, kuma za mu dawo mu ci gaba da tafiyar da ita.”