• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Friday, May 15, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Shugabancin Nijeriya: Ibo na Kano sun ce Atiku ya fi dacewa

by DAGA WAKILIN MU
February 5, 2023
in Nijeriya
0
Sarkin Ibo na Kano, Eze Ikechukwu Akpudo, tare da Alhaji Ibrahim Al-Amin (Little) a lokacin ziyarar a fadar Sarkin al'ummar Ibo na Kano

Sarkin Ibo na Kano, Eze Ikechukwu Akpudo, tare da Alhaji Ibrahim Al-Amin (Little) a lokacin ziyarar a fadar Sarkin al'ummar Ibo na Kano

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

AL’UMMAR Ibo mazauna Jihar Kano sun bayyana cewa babu wanda ya fi dacewa a zaɓa a matsayin shugaban ƙasa a zaɓen da za a yi a wannan watan kamar ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP, Alhaji Atiku Abubakar.

Sarkin Ibo na Kano, wato Eze Ikechukwu Akpudo, shi ne ya bayyana haka a madadin al’ummar tasa a lokacin da sarkin yaƙin rundunar zaɓen Atiku a Jihar Kano, Alhaji Ibrahim Ali-Amin (Little), ya kai masa ziyara a fadar sa.

Eze ɗin ya bayyana Atiku da cewa wani kadarko ne wanda ya yi aiki matuƙa wajen kawo haɗin kai a ƙasar nan.

Ya ce: “’Yan Nijeriya ba su da zaɓin da ya wuce Atiku, domin shi kaɗai ne wanda zai iya doke Tinubu a zaɓe. Ya na takara a babbar jam’iyya. 

“Wani dalilin kuma shi ne ba za mu iya goyon bayan tsarin takarar Muslim-Muslim ba. Mu na so a samu takara mai daidaito domin tabbatar da adalci ga kowa da kowa.

“Kamar yadda ku ke gani, kwanaki kaɗan ne su ka rage kafin a yi zaɓe, amma babu wani daga cikin mu da zai tashi ya koma garin su domin yin zaɓen. A nan za mu yi zaɓen tare da iyalan mu. Nan za mu tsaya, a nan mu ke harkokin kasuwancin mu.

“Addu’ar mu ita ce a yi zaɓe cikin lumana. Mun yanke shawarar cewa Atiku Abubakar kaɗai ne zai iya tunkarar matsalolin da ƙasar nan ke fuskanta a yau.

“Mu na magana ne da murya ɗaya a matsayin mu na al’umma ɗaya. Ba mu yin wata ƙunbiya-ƙunbiya a magana, kuma mu na ba mai girma Atiku tabbacin cewa shi za mu ba ƙuri’un mu. 

“Ni ɗin nan sau biyu ana zaɓa ta a matsayin kansila a Sabon Gari. Zan tattaro jama’a bakin iyawa ta don ganin Atiku ya samu nasarar lashe zaɓen da za a yi.”

A nasa ɓangaren, Ali-Amin Little ya bayyana cewa ‘yan ƙabilar Ibo mutane ne masu son zaman lafiya kuma sun yi fice a harkar kasuwanci.

Ya yi kira a gare su da su yi amfani da ƙuri’ar su yadda ya kamata domin su samu cin moriyar mulkin dimokiraɗiyya tare da sauran al’umma.

Ya ce: “Atiku Abubakar zai yi tafiya tare da dukkan ƙabilu idan ya zama shugaban ƙasa. Ƙasar nan ta yi masa komai na rufin asiri, don haka shi ma ya ke so ya mayar mata da sakayyar alheri ta hanyar samar da shugabanci mai nagarta da alfanu ga ‘yan Nijeriya.

“Hakan ne ya sa ya ke auren mace Ibo, da Bayarabiya da Kanuri, da sauran su. Shi Waziri mutum ne da ya kamata ‘yan Nijeriya su amince da shi saboda amfanuwar ƙasar da haɗin kan ta.”

Wasu waɗanda su ka take wa Al-Amin Little sawu a lokacin ziyarar sun haɗa da Dakta Auwalu Anwar, wanda shi ne mai ba Atiku shawara a ɓangaren tsare-tsare, da kuma Alhaji Bashir Kalla.

Loading

Previous Post

Tagwayen ‘yan matan Kannywood sun bayyana babbar damuwar su a rayuwa

Next Post

Zaɓen 2023: Aikin gwajin na’urar tantance masu rajistar zaɓe ya yi nasara

Related Posts

Yadda CBN ke tallabe da tattalin arzikin Nijeriya, yayin sa farashin ɗanyen mai ke faɗuwar-‘yan-bori a kasuwa
Nijeriya

Yadda CBN ke tallabe da tattalin arzikin Nijeriya, yayin sa farashin ɗanyen mai ke faɗuwar-‘yan-bori a kasuwa

November 7, 2025
Shirin ƙarfafa jari: CBN ya shawarci bankuna marasa ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji
Nijeriya

Shirin ƙarfafa jari: CBN ya shawarci bankuna marasa ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji

November 2, 2025
Bankin CBN ya yunƙuro: Naira ta hana dala numfashi mai ƙarfi a ƙarshen Oktoba
Nijeriya

Bankin CBN ya yunƙuro: Naira ta hana dala numfashi mai ƙarfi a ƙarshen Oktoba

November 2, 2025
Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje
Nijeriya

Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje

October 29, 2025
Tinubu ya yi adalci ga dukkan yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai
Nijeriya

Tinubu ya yi adalci ga dukkan yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai

August 31, 2025
Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar da Sababbin Cibiyoyin Maganin Ciwon Daji

July 24, 2025
Next Post
Shugaban INEC, Farfesa Mahmood Yakubu, a wajen aikin gwada na'urar tantance rajista a Abuja (Hoto: INEC)

Zaɓen 2023: Aikin gwajin na’urar tantance masu rajistar zaɓe ya yi nasara

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!