• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Friday, June 6, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Tallafin Ramadan: ‘Yan fim sun yaba wa Rarara

by DAGA MUHAMMAD LAWAN RANO
April 21, 2021
in Labarai
0
Tallafin Ramadan: ‘Yan fim sun yaba wa Rarara
0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

ƊIMBIN jama’a, musamman ma dai ‘yan fim, sun yaba wa fitaccen mawaƙi Dauda Adamu Kahutu (Rarara) saboda tallafin tsabar kuɗi har naira miliyan 3 da ya raba wa ‘yan fim 60 da ake ganin mabuƙata ne.

Idan kun tuna, Rarara ya raba kuɗin ne a makon jiya saboda rage wa ‘yan fim ɗin matsin da ake ciki a wannan wata na Ramadan.

‘Yan fim maza da mata ne su ka amfana da tallafin, inda aka ba kowannen su N50,000.

Wasu daga cikin waɗanda su ka ci moriyar tallafin sun bayyana farin cikin su ga mujallar Fim, kuma su ka yi wa Rarara fatan alheri.

Sun bayyana shi a matsayin wani jajirtaccen mutum mai amfani da damar sa wajen ganin ya taimaka wa mutanen da ba su da ƙarfi a cikin wannan masana’anta ta Kannywood.

Sai dai daga cikin waɗanda su ka amfana sun bayyana cewa wannan ba shi ne karo na farko da mawaƙin ke taimaka wa ‘yan fim ba.

A tattaunawar sa da mujallar Fim, dattijo Alhaji Isah Bello Ja wanda ya na ɗaya daga cikin waɗanda su ka amfana da tallafin, ya bayyana cewa tallafin ya zo a daidai lokacin da ake da buƙatar sa.

Ya ce, “Wannan tallafi ya zo a daidai lokacin da ake da buƙata. Haƙiƙanin gaskiya duk wanda aka ba wa tallafin nan ya na da buƙatar sa, duk da cewa ba wannan ne na  farko ba, don watanni biyu da su ka gabata ya bada tallafin dubu hamsin-hamsin ga wasu mutane, kuma har da ni a ciki, kuma wannan ɗin ma ya sake bada tallafin har da ni a ciki.

“Kun ga ban da mutumin kirki mai tsoron Allah, ko wanda ya ke neman gudunmawa daga Allah, ba wanda zai yi haka.

“Ba abin da za mu ce da Dauda Kahutu Rarara sai dai mu yi masa fata na alkairi. Allah ya saka masa da alkairi. Allah ya daɗo wasu mutane a wannan masana’antar tamu ta Kannywood irin su Dauda Kahutu Rarara.

“Kuma wallahi ni da gaske na ke yi, ya tallafa min kuma ina buƙatar tallafin. Na gode masa. Allah ya biya shi.”

Shi ma a nasa ɓangaren, mawaƙi Bello Ibrahim (Billy O) ya tabbatar wa da mujallar Fim cewa, ”Na karɓi dubu hamsin kamar yadda aka umarta, wanda daga garin Fatakwal aka yi min waya aka ce Rarara ya bada kuɗi a ba wa jarumai kuma har da suna na a ciki. Kuma alhamdu lillahi furodusa Maishadda ya same ni ya ban N50,000 kuma na karɓa a hannu na.”

Billy O ya kuma yi jan hanakali kamar haka: “Kamar yadda wannan mawaƙi ya bada wannan tallafin, kamata ya yi a ce mu ma mu na taruwa mu na taimaka wa mutane, musamman ‘yan Arewa, to da za a samu ci gaba sosai.

“Kuma hakan da ya yi ba ni kaɗai ya taimaka wa ba, mu na da yawa a Kannywood. Ka ga zai samu lada. Gaskiya na ji daɗi. 

“Kuma shawara shi ne ina ma dukkan mu shawara mu dinga yin haka.”

Auwalu Zomuleƙa, wanda shi ma ya amfana da kuɗin tallafin, ya bayyana tallafin a matsayin wani abu da aka saba yi masa, ba wai shi ne karo na farko ba.

 “Na ji daɗi sosai. Kuma da man ai shi ya saba yin irin wannan abubuwan, domin akwai wani lokaci da na yi jiyya kuma ya na ɗaya daga cikin waɗanda su ka ba ni babbar gudunmawa. Na ji daɗi sosai. 

A hagu: Isa Bello Ja. Daga sama: Billy O, Asma’u Sani da Ladidi Tubless

“Allah ya saka masa da alkairi, kamar yadda ya ke taimaka wa al’umma, shi ma Allah ya taimake shi, sannan Allah ya yi ba shi ninkin abin da ya yi mana.”

Su ma matan da su ka amfana da tallafin sun bayyana farin cikin su dangane da hakan tare da yin jinjina ga mawaƙin.

Ladidi Abdullahi (Tubeless) ta bayyana wa mujallar Fim cewa, Lokacin da aka kira ni ake sanar da ni, ina zaune ne a cikin gida tare da ‘yan’uwan mu aka kira ni a waya aka sanar da ni, aka ce, ‘Kin ga sunan ki a cikin waɗanda za a ba wa dubu hamsin.’ Na ce, ‘Na me?’ Aka ce na tallafin Rarara na azumi. Waallahi sai da na yi ihu don jin daɗi duk kuma da cewa wannan ba shi ne tallafi na farko da ya ba ni ba!

“Sannan waɗanda mu ke tare da su a lokacin da aka gaya min su ka ji sai da na yi musu alkairi su ma, kuma su ka gode masa su ka ji daɗi. To ka ga wannan ai abin alfahari ne.”

Kuma maganar gaskiya, da na zata Rarara ya manta da ni, don na ma cire rai, amma da aka ba ni wannan tallafi kuma aka ba ni na baya shi ma dubu hamsin, na ce gaskiya wannan mutumin ya na tare da mu, bai manta da mu ba ashe.

“Na gode. Ubangiji Allah ya masa sakayya da gidan Aljanna.”

Ita ma Asma’u Sani ta bayyana farin cikin ta, inda ta yi wa Rarara addu’o’in samun buɗi a rayuwar sa.

Sai dai kuma wasu jarumai da su ka amfana da tallafin sun noƙe sun ƙi yin magana lokacin da wakilin mu ya tuntuɓe su don jin ta bakin su game da wannan abin alheri da Rarara ya yi.

Loading

Tags: Asma'u SaniAuwalu ZomulekaBilly ODauda Kahutu RararaDauda RararaIsa Bello JaLadidi TubelessRamadan 2021Tallafin azumi
Previous Post

Ramadan: Zan taimaka wa mutane sama da 5,000 a wannan wata – Rasheeda Maisa’a

Next Post

2023: INEC ta yi wa sassan ta na cikin gida garambuwal

Related Posts

An naɗa Shehu Hassan Kano shugaban riƙo na MOPPAN
Labarai

An naɗa Shehu Hassan Kano shugaban riƙo na MOPPAN

June 3, 2025
MOPPAN ta ba gwamnan Kebbi lambar yabo a madadin ‘yan fim
Labarai

MOPPAN ta ba gwamnan Kebbi lambar yabo a madadin ‘yan fim

June 2, 2025
Ƙungiya ta ja kunnen gwamnatin Kano kan dakatar da finafinan Kannywood 22
Labarai

Ƙungiya ta ja kunnen gwamnatin Kano kan dakatar da finafinan Kannywood 22

May 20, 2025
Hukuma ta rufe gidajen gala a Kano har sai bayan Ramadan
Labarai

Gwamnatin Kano ta dakatar da haska finafinan Kannywood 22 a intanet da talbijin 

May 19, 2025
Labarai

Gwamnan Kano ya ɗauki nauyin ‘yan Kannywood 5 zuwa Hajjin bana

April 17, 2025
Sabuwa, matar Ɗanmaraya Jos, ta rasu
Labarai

Sabuwa, matar Ɗanmaraya Jos, ta rasu

March 28, 2025
Next Post
2023: INEC ta yi wa sassan ta na cikin gida garambuwal

2023: INEC ta yi wa sassan ta na cikin gida garambuwal

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!