• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Monday, June 30, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Walle-Walle a tsohuwar gwamnatin Matawalle a Zamfara

by DAGA WAKILIN MU
October 30, 2023
in Nijeriya
0
Bello Matawalle da ɗaya daga cikin gidajen da ba a gama ba

Bello Matawalle da ɗaya daga cikin gidajen da ba a gama ba

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

A BINCIKEN wata harƙalla bayan ta ginin filin jirgi a Zamfara, gwamnatin jihar ta fitar da sababbin hujjoji waɗanda ke fallasa yadda tsohon gwamna kuma Ƙaramin Ministan Tsaro a yanzu, Bello Matawalle, ya rattaba hannu kan fitar da biliyoyin kuɗi don aikin gidajen saukar gwamna.

Tsohuwar gwamnatin ta Matawalle ta ƙirƙiri aikin ginawa tare da sayo kayayyaki don gidajen saukar gwamna a ƙananan hukumomi 14 da ake da su a jihar.

Wata takardar sanarwar manema labarai da Kakakin Gwamnan Zamfara, Sulaiman Bala Idris, ya fitar a ranar Lahadi a Gusau ta bayyana cewa takardun da aka fitar su na cikin jerin salsalar fallasa irin ɓarnar da Matawalle ya tafka a lokacin ya na gwamna.

Ya ƙara da cewa gwamnatin Dauda Lawal ba za ta yi shiru ko kawar da kai kan satar rashin imani da tsohuwar gwamnatin ta aikata ba, musamman inda aka bayar da ayyuka, aka kwashi biliyoyi kuma aka yi watsi da ayyukan.

Sanarwar ta ci gaba da cewa: “Ya saɓa wa ƙa’idar gudanarwa a tsarin gwamnati, haka kawai mutum ya biya kuɗi ɗari bisa ɗari kan kwangilar da ba a fara aiwatarwa ba. 

“Za ka taras da irin waɗannan kwangiloli, ga su nan birjik an sace kuɗaɗen al’umma da sunan yin su.

“Za mu bibiyi duk waɗanda suka tafka irin wannan sata, domin mu dawo wa da al’umma haƙƙin su.

“Daga cikin irin waɗannan ayyuka da tsohuwar gwamnatin Bello Matawalle ta kwashe kuɗaɗe da sunan su akwai batun ginin gidajen saukar gwamna a Ƙananan Hukumomi 14 na jihar, wanda tun kafin ma a fara aikin aka kwashe biliyoyi da sunan kuɗin sayo kayan gidajen.

“Bello Matawalle ya fitar da kuɗi don biyan mafi yawa daga cikin ‘yan kwangilar. Misali, ya tura wa kamfanin BES BELMON Nigeria Limited Naira 1,966,035,160.00 a ranar 27 ga Disamba, 2021 domin aikin katangewa, sayo kayayyakin cikin gida, da sanya wutar lantarki ga waɗannan gidajen saukar gwamna guda 14, tun ma kafin a fara aikin su.

“An biya gaba ɗaya kuɗaɗen aiki ga ‘yan kwangilar da ke aikin gina gidajen na saukar gwamna a ƙananan hukumomin Ƙaura Namoda, Zurmi, Bakura, Maradun, Bukkuyum, Bunguɗu da Gummi, tun kafin a fara aikin.

“A ranar 30 ga Afrilu, 2020 gwamna ya rattaba hannu don a fitar da kuɗi Naira 324,410,211.00 ga kamfanin SWAT AGA Construction Limited domin a gina gidan saukar gwamna a Ƙaramar Hukumar Ƙaura Namoda. An fitar da wannan kuɗin ne daga Ma’aikatar Kananan Hukomomi da Masarautu. 

“Haka kuma a ranar dai 30 ga Afrilu, 2020 ɗin an sake fitar da naira 324,410,211.00 ga kamfanin na SWAT AGA Construction Limited, a matsayin kuɗin aikin ginin gidan saukar gwamna a Ƙaramar Hukumar Zurmi.

“Ƙarin abin haushi, wannan kamfanin na BES BELMON wanda aka biya sama da biliyan ɗaya don sayo kayan gidajen da ba a kammala ginawa ba, shi ne a ranar 30 ga Afrilu, 2020 aka sake fitar da 324,410,211.00 aka ba shi don ya gina gidan saukar gwamna a Ƙaramar Hukumar Maradun.

“Mu na so a fahimci irin badaƙalar da kamfanin BES BELMON Nig. Limited ke ciki, musamman tarayyar da ya yi wurin fitar da kuɗaɗe daga baitilmalin Jihar Zamfara ba tare da ƙa’ida ba.”

Sanarwar ta ci gaba da cewa, “A dai ranar 30 ga Afrilu, 2020 ne Bello Matawalle ya sake fitar da naira 324,410,211.00 ga BES BELMON don gina gidan saukar gwamna a Ƙaramar Hukumar Bukkuyum. Abin tambayar shi ne, wanene ke da wannan kamfani na BES BELMON?

“Duk dai a ranar 30 ga Afirilu, 2020, Bello Matawalle ya sa aka fitar da naira 324,410,211.00 aka ba BES BELMON a matsayin kuɗin gina gidan saukar gwamna a Ƙaramar Hukumar Bunguɗu.

“Gwamnatin Zamfara za ta ci gaba da bankaɗo sama da faɗi da rashin gaskiyar da aka tafka, ba don komai ba sai domin tabbatar da adalci. 

“Saboda haka ne ma mu ke kira ga kamfanin BES BELMON Nigeria Limited da ya gaggauta dawo wa gwamnatin da naira 1,966,035,160.00 da Bello Mohammed Matawalle ya biya shi ba tare da ƙa’ida ba. Aikin ceto mu ka zo yi, ba za mu ɗaga wa maha’inta ƙafa ba.” 

Haka sanarwar ta bayyana a shafin Facebook na Kakakin Yaɗa Labaran Gwamna Dauda Lawal, wato Sulaiman Idris.

Loading

Previous Post

Bayan nasara a Kotun Ƙoli, Shugaba Tinubu zai ci gaba da aikin gina nagartacciyar ƙasa – Idris

Next Post

Gwamnatin Tinubu ba za ta ƙaƙaba wa jama’a takunkumin hana magana ba – Minista

Related Posts

Nijeriya

Gwamnatin Tarayya ta bada tabbacin akwai tsaro a Abuja duk da gargaɗin da Amurka ta ba matafiya

June 23, 2025
Kiran Gwamnatin Tarayya ga ‘yan jarida: Ku zama jigo wajen gina dimokiraɗiyyar Nijeriya
Nijeriya

Kiran Gwamnatin Tarayya ga ‘yan jarida: Ku zama jigo wajen gina dimokiraɗiyyar Nijeriya

June 21, 2025
Ministan Yaɗa Labarai ya yaba wa Hafsoshin Soji kan cigaban da aka samu a fannin tsaron ƙasa a shekaru biyu
Nijeriya

Ministan Yaɗa Labarai ya yaba wa Hafsoshin Soji kan cigaban da aka samu a fannin tsaron ƙasa a shekaru biyu

June 20, 2025
Nijeriya tana kan hanyar farfaɗowar tattalin arziki da dawo da martabar ƙasa — Minista
Nijeriya

Nijeriya tana kan hanyar farfaɗowar tattalin arziki da dawo da martabar ƙasa — Minista

June 13, 2025
Gwamnatin Tarayya za ta tallafa wa yekuwar rigakafin cutar ƙyandar Jamus
Nijeriya

Gwamnatin Tarayya za ta tallafa wa yekuwar rigakafin cutar ƙyandar Jamus

June 4, 2025
Tinubu ya tura wakilai zuwa Neja kan ambaliyar Mokwa da ta halaka sama da mutum 150
Nijeriya

Tinubu ya tura wakilai zuwa Neja kan ambaliyar Mokwa da ta halaka sama da mutum 150

May 31, 2025
Next Post
Alhaji Mohammed Idris (a hagu) a lokacin tattaunawar sa da gidan talbijin na Arise... A daren Asabar

Gwamnatin Tinubu ba za ta ƙaƙaba wa jama'a takunkumin hana magana ba - Minista

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!